RAMADAN KARIM: 01-1447
__________

Ma sha Allah, Alhamdu lillah. Allah ya kawo mu watan Ramadan mai albarka. Bari mu yi wa juna nasiha:
Allah (swt) a cikin Alƙur’aninsa mai girma, Suratul Bayyinah 98:5 ya ce: “Ba a umarce su ba sai su bauta wa Allah suna masu tsarkake addini gare Shi.”
Haka kuma a hadisi mai lamba 1907, a Sahih al-Bukhari da Muslim, sun ruwaito Manzon Allah (saw) yana cewa: “Lallai kowane aiki yana tare ne da niyya.”
Wannan shi ke tabbatar mana da cewa Allah yana karɓar aiki ne idan an yi shi don Shi kaɗai. Don haka nu gyara niyyarmu a duk abin da muke aikatawa. A wannan wata, mu yawaita ayyukan alheri komai ƙanƙantarsu. Allah sa mu dace, Amin.
__________













