Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (5)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
√ Wasu Muggan Manufofin Ƙungiyar Hausawan Bogi:
Malam Lamiɗo Suleiman Dungal, ɗaya daga cikin masana masu nazarin illolin da ke tattare da Ƙungiyar Hausawa Zalla ko kuma Hausawan Bogi, ya zayyano wasu daga cikin munanan ƙudurori da manufofinsu. Daga ƙarshe dai nazarin nasa ya tabbatar mana da cewa ita wannan karkatattar ƙungiya, an tsira ta ne da mugun ƙudurin tarwatsa Arewa da al’ummarta.
A wannan nazari nasa mai ƙima, Malam Lamiɗo ya kawo wasu bambance-bambancen da ke tsakanin wannan ƙungiya ta Hausawa Zalla da sauran ƙungiyoyin ƙabilu, waɗanda aka kafa da nufin bunƙasa al’ummarsu da taimakon juna. Ga bayanin nan daki-daki:
√ A yayin da sauran ƙabilu suke kafa ƙungiya domin inganta rayuwar al’ummarsu, ba wai don ware kansu daga sauran al’umma ba, su Hausawan Bogi sun bayyana ƙarara cewa babu ruwansu da wata ƙabila sai tasu. Alhali sauran ƙungiyoyin suna bai wa abokan zaman rayuwa damar musharaƙa da juna, ba tare da la’akari da ƙabila ba.
√ Shugabannin sauran ƙungiyoyin ƙabilu ba su kafirta ko cin mutuncin wata ƙabila, sai dai su yi aiki tuƙuru don ci gaban ƙabilarsu. Amma ƙungiyar Hausawa Zalla tana yawan rikici da wasu ƙabilu, musamman ma Fulani, waɗanda take zagi da la’anta tare da jan hankalin al’umma domin a tsane su kuma a ƙyamace su.
√ Ƙungiyoyin ƙabilu na gaskiya suna da bayyanannun shugabanni kuma ba sa ɓoye asali ko shaidarsu. Suna aiki tare da kowace gwamnati. Amma a ɓangaren Hausawa Zalla kuwa, ba a san shugabanninta ba, ba su fitowa fili. Babu abin da suke yi sai dai su riƙa yaɗa saƙonni a kafafen sada zumunta, domin kawo ruɗani. Saƙonnin nasu suna ɗauke da gubar ƙabilanci da cin zarafi da zage-zage.
√ Masu kiran kansu Hausawa Zalla, ba su da ofis kuma ba za ka samu wanda ya fito fili ya ce shi memba ba ne. A kafafen sada zumunta ma suna ɓoye sunayensu na ainihi, suna rufe bayaninsu (profile), ta yadda mutum ba zai fahimci ko su wane ne ko adireshinsu ba.
√ Ƙungiyar Hausawa Zalla, yawancinsu ma ba Musulmi ba ne, domin shugabarsu ta fito a kafafen sada zumunta tana cin mutuncin Musulunci, tana cewa ƙabilanci ya fi addini muhimmanci. Tana faɗin cewa hatta kashi ko najasar Bahaushe ta fi Musulunci.
√ Wata babbar alama ko tambarin ‘yan Ƙungiyar Hausawa Zalla ita ce, tsana da ƙiyayya da Musulunci da Musulmi. Duk wani malamin Musulunci, tun daga Mujaddadi Shehu Ɗanfodiyo zuwa malamanmu na zamanin nan, babu wanda ba su ci wa zarafi, suka zage shi ba. Kuma za ka ga suna goyon bayan masu gwagwarmayar kafa ƙasar Inyamurai ta Biyafara kuma suna zuzuta wutar gaba da goyon bayan ƙabilun Middle Belt a kan Fulani.
√ A hannu ɗaya, ƙungiyoyin Fulani da makamantansu da aka kafa don maslahar rayuwa, ƙungiyoyi ne na makiyaya da al’umma baki ɗaya. Duk wanda ke kiwo, ko daga wace ƙabila yake, ana iya ba shi dama ya shiga cikinsu, har ma ya shugabanci ƙungiyar. Wannan ne ya sa a cikin shugabannin ƙungiyoyin Fulani ake samun waɗanda ba Fulani ba. Haka ma a ƙungiyoyin manoma ko mahauta, duk za ka samu bayaninsu da ayyukansu a bayyane kuma suna da rijista da hukumomin ƙasa, alhali ita wannan ƙungiya ta Hausawa Zalla, ba ta da rijista, ba ta da ofis kuma ba a san membobinta da shugabanninta ba a zahiri. Wasu ma ba ‘yan Najeriya ba ne kuma ba a nan suke zaune ba.
Wani babban abin lura a nan shi ne, babu wanda zai hana kowace ƙabila kafa ƙungiya domin kare haƙƙin al’ummarta, komai ƙanƙantarta, ballantana babbar ƙabila irin ta Hausawa. Matsalar ita ce, ba a kafa ƙungiya da niyyar cin mutuncin wata ƙabila ko addini. Ba a kafa ƙungiya ba tare da bayyanannen shugaba ɗaya ba. Dole ƙungiya ta kasance an san ta kuma tana da rijista da gwamnati kuma tana da ofis kuma ayyukanta su kasance bayyanannu ga jama’a, ba a ɓoye ba.
A nan za mu ɗiga aya, tare da fatan sake haɗuwa a tsokaci kashi na 6. Da fatan muna fahimtar illolin wannan karkatattar ƙungiya da muggan manufofinta na kassara al’ummar Arewa.
__________













