Sakatare Ibrahim Dasuƙi Abubakar: Al’ummar Malumfashi Ta Samu Ƙaruwa
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

_______________
A ranar Asabar da ta gabata (18-10-2025), sanarwa ta gabata daga mai girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa, inda ya naɗa muhimman mutane takwas a matsayin Manyan Sakatarori (Permanent Secretaries). Cikin waɗannan mutane takwas, har da Alhaji Ibrahim Dasuƙi Abubakar (Ɗan Madawakin Galadiman Katsina).
Wane Ne Ibrahim Dasuƙi Abubakar?
Bayan da al’umma suka ji an ambata sunansa a matsayin Babban Sakatare, wasu sun taya shi murna da addu’ar Allah taya shi riko. Wasu kuwa, musamman waɗanda ba su san shi ba, tambayoyi suka yi ta jefawa: Shin shi ɗan wane gari ne? Daga wace ƙaramar hukuma yake?
A cikin masu tambayoyin nan, akwai masoya, waɗanda suna tambaya ne kawai domin neman sani, ba da wata mummunar manufa ba. Haka kuma akwai maƙiya kuma mahassada, waɗanda ba kawai tambaya suke ba, har ma suna ƙoƙarin kore shi daga ƙaramar hukumarsa.
Shi dai Malam Dasuƙi, cikakke kuma halaltaccen ɗan Ƙaramar Hukumar Malumfashi ne, a Jihar Katsina. Haka kuma, ta ɓangaren uwa da uba, shi jinin Sarautar Galadancin Katsina ne.
Ta ɓangaren uba, Ibrahim Dasuƙi Abubakar jikan-jika ne ga marigayi Galadiman Katsina Abu, wanda ya yi mulki a shekarar 1925. Wasu daga cikin ‘ya’yan da shi Galadiman ya haifa, sun haɗa da: 1-Kogo Abdullahi (mahaifin marigayi Galadima Mamman Nasir). 2-Alhaji Ibrahim Na-Yabiri, Madawakin Maigora kuma mahaifin shi Ibrahim Dasuƙi. 3-Alhaji Garba Ɗangoggo. 4-Alhaji Umaru Chajinas (ya zauna a Unguwar Galadanci Katsina). 5-Alhaji Alu Gizanda (mahaifin Dokta Halima Adamu). 6-Alhaji Abdulƙadir ‘Yammama, Danejin Katsina-I (mahaifin Danejin Katsina-II). 7-Alhaji Maishanu (mahaifin Sarkin Fadan Galadiman Katsina). 8-Alhaji Ahmed Nashehu (mahaifin Zayyana Ahmed, tsohon Kwamishina). 9-Alhaji Yusuf Audi (mahaifin Justice Abdullahi Yusuf).
Ta ɓangaren uwa kuwa, Ibrahim Dasuƙi jikan-jika ne ga marigayi Magajin Garin Malumfashi Aliyu. Cikin ‘ya’yansa, akwai Ruwan Sanyi Abdullahi da kuma Hajiya Karime.
Hajiya Karime, kakar Ibrahim Dasuƙi, ita ce ta haifi waɗannan ‘ya’yan: 1-Alu Gizanda. 2-Alhaji Abdulƙadir ‘Yammama. 3-Alhaji Maishanu. 4-Alhaji Sanin Gora (Magajin Gora). 5-Alhaji Tukur Ƙofar Gardi (mahaifin Anas Tukur). 6-Hajiya Indo (mahaifiyar Zailani Tijjani. 7-Alhaji Usman Mai-Nagari. 8-Hajiya Hassana. 9-Hajiya Hassana (mahaifiyar Ibrahim Dasuƙi Abubakar).
Mahaifin Sakatare Ibrahim Dasuƙi Abubakar, shi ne Alhaji Ibrahim Na-Yabiri kuma ga sunayen ‘ya’yansa maza da ya haifa: 1-Alhaji Lawal Nadadaye. 2-Alhaji Abdullahi Ibrahim (marigayi Madawakin Maigora kuma mahaifin KB-Lama). 3-Alhaji Usman Jariri. 4-Alhaji Abubakar Mai-Ɗanja (Member, State Assembly Commission). 5-Farfesa Adamu Ibrahim Malumfashi (Sashen Harsunan Najeriya, Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya). 6-Alhaji Aliyu Ibrahim. 7-Alhaji Ibrahim Dasuƙi Abubakar. 8-Yusuf Ibrahim.
Wannan shi ne cikakken jadawalin iyayen Babban Sakatare Ibrahim Dasuƙi Abubakar ta ɓangaren uwa da uba. Shi cikakken ɗan Ƙaramar Hukumar Malumfashi ne. Duk mai shakka sai ya daina.
A yayin da ya samu wannan babban matsayi a Gwamnatin Jihar Katsina, muna taya shi murna, tare da addu’ar Allah ya taya shi riko. Allah ya sa aikinsa ya zama mai amfani ga al’ummar Malumfashi, Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya. Amin-Summa-Amin.
_______________












