Katsinawa Suna Murna Da Ɗaukakar Da Maryam Idris Ta Samu
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
A wata sanarwa ta musamman daga Fadar Gwamnatin Jihar Katsina, Gwamna Radda, a madadin al’ummar jihar, ya yaba tare da taya murna da naɗin Maryam Idris a matsayin Wakiliyar Najeriya a Ƙungiyar Ƙasashe Masu Arziƙin Man Fetur ta Duniya (OPEC).
Maryamu, wadda a halin yanzu take riƙe da muƙamin Darakta-Janar a Kamfanin NNPC Trading Limited, ‘yar asalin Jihar Katsina ce.
Sanarwar, wacce Sakataren Watsa Labarai na Gwamnan, Malam Ibrahim Kaulah Mohammed ya sanya wa hannu, ya ce, yayin da yake bayani a kan wannan naɗi, Gwamna Radda ya bayyana shi a matsayin shaida ga ingancin ƙwararrun mutanen da Jihar Katsina ke ci gaba da samarwa don hidima ga ƙasa da ƙetare.
“Muna alfahari da cewa ‘ya mace daga Katsina ta samu ci gaba, har aka amince da ita, ta wakilci Najeriya a irin wannan babbar ƙungiya mai martaba a faɗin duniya,” in ji Gwamnan.
Ya yi amanna da cewa Maryamu za ta yi amfani da ƙwarewarta a harkar mai da iskar gas wajen kare muradun Najeriya a Ƙungiyar OPEC.
Gwamnan ya kuma lura da cewa wannan naɗi yana nuna jajircewar Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na naɗa ‘yan Najeriya masu cancanta a muhimman muƙamai, ba tare da la’akari da jihar da suka fito ba.
Gwamna Radda ya yi wa Maryamu fatan nasara a sabon aikinta, tare da ba ta shawarar cewa, ta ci gaba da kasancewa jakadiya tagari ga Jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya.
_______________













