TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (7)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Jama’a masu bibiyar wannan rahoto mai kama da muƙala, wannan shi ne rahoto kashi na 7, dangane da wannan babban taro da aka gudanar na Malumfashi Facebook Connect. Idan ba mu mance ba, an gudanar da taron ne a ranar Lahadi, 12-12-1446 (Hijiriyya), 08-06-2025 (Miladiyya).
A wannan rahoto, kamar yadda muka bayyana a ƙarshen kashi na 6, cewa a yau za mu tattauna ne game da Alhaji Jibrin Sama’ila (Jibson), wanda shi ma ya kasance cikin zaratan mutanen da aka karrama da kambi, a yayin taron.
√ Wane Ne Jibrin Sama’ila (Jibson)?
Babu shakka Allah ya albarka Malumfashi da zaratan mutane masu kishi, waɗanda kuma Allah ya azurta da dukiya mai albarka tun suna da ƙuruciya. Alhaji Jibrin, kamar abokinsa Injiniya Muntari Sagir, shi ma matashin attajiri ne, wanda dukiyarsa ke amfanar al’ummar Malumfashi da kewaye.

A takaice dai, an haifi Jibrin Jibson a Unguwar Sodangi, Malumfashi a shekarar 1980. Ya yi dukkan karatunsa na firamare da sakandare, duk a Malumfashi. Daga nan ne ya shiga gwagwarmayar neman abin rayuwa.
Jibson ya taso cikin ƙwaƙuduba da faɗi tashin neman na kansa. Mutum ne mai ƙoƙarin nema, tun yana ƙarami. Ya yi ayyuka da sana’o’i iri daban-daban. Kamar yadda bincike ya tabbatar, ya taɓa yankar ciyawar dabbobi yana sayarwa. Akwai lokacin da ya riƙa shiga dazukan Malumfashi, yana saro itace, yana sayarwa.
Ya yi sana’o’i iri-iri, duk domin ya rufa wa kansa asiri a rayuwa. Waɗannan kuwa sun haɗa da sana’ar sayar da fetur da dizal a bakin titi. Ya yi sana’ar ruwan leda da yogot. Allah ya tarfa wa nemansa albarka, inda a halin yanzu yake da kamfanin Nasaka/Jibson Investment. A ƙarƙashin kamfanin, yana da gidajen mai, yana noman zamani, kamar kuma yadda yake gudanar da kwangilar gine-gine da sauransu.
√ Abin Da Ya Sa Aka Karrama Shi:
A wannan taro na Malumfashi Facebook Connect, an zaɓi mutane ne masu mutunci, masu amfanar da al’umma, aka karrama su. Alhaji Jibrin Jibson, babu shakka ya cancanci wannan karramawa, kamar sauran waɗanda aka karrama a ranar. Dalili kuwa shi ne, ta hanyar sana’arsa, ya yi sanadiyyar koya wa matasan Malumfashi sana’o’in dogaro da kansu. Ya koya masu cewa su tashi su nemi na kansu cikin ƙoƙari da jajircewa.
Ta fannin taimakon al’umma, musamman ma raunana da mabuƙata, Jibson a gaba-gaba yake. Yana da zumunci da taimakon ‘yan uwa da abokai. ‘Yan uwansa na jini da abokansa su ne manyan shaidu. Duk wani da ya rayu ko yake kan rayuwa a Unguwar Sodangi Malumfashi, zai kasance mai shaidar alheri ga Jibson. Mutum ne shi kuma mai ƙanƙan da kai – ba ya da girman kai ko toƙabo da dukiyar da Allah ya ba shi. Haka kuma ba ya yayata kyauta ko taimakon da yake wa mutane.

Wani babban al’amari game da shi kuma shi ne – Jibson mutum ne mai kishin addini. Taimakon masallatai da masallata da malaman addini, halinsa ne. Akwai makarantar islamiyya mai suna HIDAYA, a Unguwar Sodangi Malumfashi, a duk lokacin da aka zo bikin yaye ɗalibai, shi ke saya masu sabbin suturu, maza da mata. Wani lokacin ana yaye ɗaliban da suka kai 100 ko sama da haka.
√ Ƙarin Bayani:
A wata ganawa da na yi da shi, kwana biyu da kammala taron nan, na tambaye shi cewa, shin mene ne yake ba shi karsashi da ƙwarin gwiwar taimakon al’umma? Ya amsa da cewa:
“Maganar gaskiya, babban abin da ke mani ƙaimi kuma nake son taimakon mabuƙata shi ne, na taso cikin wahala, na ɗanɗani raɗaɗin talauci. Kan haka na san irin raɗaɗin da mabuƙata ke ciki. Dalili ke nan, idan na wayi gari ba tare da na taimaka wa mabuƙata ba, ba na jin daɗi.”
Jibson ya ƙara da cewa: “Na yi imani da Allah, cewa shi ke bayarwa kuma shi ke hanawa. Ni, Allah ya ba ni kuma shi ya ce yana son masu taimakon bayinsa. Dalili ke nan ya sa nake bayarwa kuma ina ganin falala da buɗi daga Allah, a sakamakon wannan taimako da nake bayarwa ga mabuƙata.

Jama’a, wannan shi ne Alhaji Jibrin Sama’ila (Jibson) a taƙaice. Idan Allah ya kai mu rahoto na gaba, kashi na 8, za mu kawo bayani game da Dr. Injiniya Tukur Hassan Tingilin, wanda shi ma aka karrama a yayin wannan taro na Malumfashi Facebook Connect.
_______________
Bashir Malumfashi, shi ne Editan Mujallar Taskar Gizago a intanet













