• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, May 2, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

ƘUNGIYAR HAUSAWA ZALLA: TA INA ZA A FARA KUMA DA WACE MANUFA? (5)

MUƘALA

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
May 24, 2025
in Gizago
0
ƘUNGIYAR HAUSAWA ZALLA: TA INA ZA A FARA KUMA DA WACE MANUFA? (5)

Hausawa Da Fulani 'Yan Uwan Juna Ne

39
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

ƘUNGIYAR HAUSAWA ZALLA: TA INA ZA A FARA KUMA DA WACE MANUFA? (5)

Daga Yahuza Malumfashi

Related posts

Rantsuwa Da Ƙur’ani: Martani Ga Shugaban Hausawan Bogi

Rantsuwa Da Ƙur’ani: Martani Ga Shugaban Hausawan Bogi

April 20, 2026
Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

April 16, 2026
Hausawa Da Fulani ‘Yan Uwan Juna Ne

Ko Me Ya Sasm ‘Ya’Yan Ƙungiyar Hausawa Suke Suka Da Zagin Ɗanfodiyo (RTA)?

Assalamu alaikum, ya ku ‘yan uwa masu bibiyar muƙalar nan da haƙuri. A yau za mu ci gaba da tattauna al’amarin ‘ya’yan Ƙungiyar Hausawa Zalla.

Kamar yadda na faro bayani a muƙalar nan Kashi na 4, yau ma zan ɗora da tambayar da ta danganci Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo (RTA), wanda ingantaccen tarihi ya yi masa adalci, a matsayin wani babban jigon da ya jaddada Musulunci kuma ya kafa babbar daular da ta yi shuhura a Afrika ta Yamma.

Har yanzu dai muna tambaya, shin wane dalili ne ya sanya masu ƙumajin kafa Ƙungiyar Hausawa Zalla suke sukar wannan bawan Allah kuma suke ci masa mutunci, suke ƙirƙirar tarihin ƙarya, suna jingina masa?

Ga duk mai tu’ammali da kafafen Soshalmidiya, tabbataccen abu ne cewa, zai ga yadda ‘ya’yan ƙungiyar nan suke zaƙewa wajen cin mutunci ga Mujaddadi da dukkan waɗanda suke da dangantaka da shi, tun daga kan ƙabilarsa ta Fulani; har zuwa kan Sarkin Musulmi na yanzu, Mai Alfarma, Sultan Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar III, CFR. Haka kuma, mutum zai ga yadda suke kushe addinin Musulunci, kai tsaye ko kuma a kaikaice.

Ko a makon nan da ya gabata, mun ci karo da wani bidiyo yana yawo, inda wata mai suna Kaltume, wacce take kwarmata cewa ita ce shugabar wannan ƙungiya ta Hausawa Zalla ta duniya baki ɗaya, tana furta baƙaƙen maganganu game da Musulunci da Musulmi.

A bidiyon, ta fito ƙarara tana faɗin cewa a yanzu ita kafura ce, ta bar Musulunci. Har ma ta yi kira ga Hausawa, wai daga yanzu su daina amfani da kalmomin Larabci wajen sallama. Ta ce, maimakon a riƙa cewa “Assalamu alaikum…” sai dai su riƙa cewa “Gafaran ku dai…” Wannan ke ƙara nuna maka cewa, lallai wannan ƙungiya ba don ci gaban al’umma aka nufa da ita ba.

Ya ku ‘ya’yan Ƙungiyar Hausawa Zalla, an fa yi walƙiya, duk wani mai hankali ya gano wallenku. Babbar manufarku dai ita ce, haddasa fitina tsakanin al’umma, musamman al’ummar Hausawa da Fulani, waɗanda a halin yanzu ‘yan uwan juna ne ta fuskar zamantakewa da addini da ma auratayya tsakanin juna.

Babban burinku shi ne, ku wargaza al’ummar Arewa, ku haddasa gaba da tsanar juna tsakanin al’umma. Burinku ne kuma ku yaƙi addinin Musulunci da Musulmi. Dalili ke nan kuka ɓullo da alayen kishin Hausawa, domin ku yi ɓadda-bami, ko kuma abin da ake kira”BA-ZATA,” domin ku shammaci mutane, ba tare da sun yi aune ba.

Jama’a, yau ma a nan zan dakata. Ina sha Allahu a kashi na 6, zan ci gaba, inda za mu amsa tambayar cewa; shin Mujaddadi Ɗanfodiyo, taimakon Hausawa ya yi ko cutar da su ya yi?

A ci gaba da bibiyar mu da haƙuri. Ku huta lafiya.
_______________
Bashir Malumfashi, shi ne Editan Mujallar Taskar Gizago (online).
_______________
Kuma muna maraba da sharhi ko tsokaci ko tambaya a kan wannan maudu’i a Comment Section.
_____
👇

Previous Post

Nazari Da Sharhin Littafin “Sai An Yi Da Gaske”

Next Post

Ya Kamata Marubuta Mu Karkata Alƙalaminmu Ga Matsalolin Al’umma

Related Posts

Rantsuwa Da Ƙur’ani: Martani Ga Shugaban Hausawan Bogi
Gizago

Rantsuwa Da Ƙur’ani: Martani Ga Shugaban Hausawan Bogi

April 20, 2026
Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa
Gizago

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

April 16, 2026
JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista
Gizago

JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

April 3, 2026
Next Post
Ya Kamata Marubuta Mu Karkata Alƙalaminmu Ga Matsalolin Al’umma

Ya Kamata Marubuta Mu Karkata Alƙalaminmu Ga Matsalolin Al'umma

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

A REVIEW: Nigeria @ 63 Independence Day Anniversary Celebration

A REVIEW: Nigeria @ 63 Independence Day Anniversary Celebration

October 13, 2023
Yau Take Juma’a: Allah Ka Albarkace Mu

Yau Take Juma’a: Allah Ka Albarkace Mu

December 5, 2025
TSOKACINMU NA YAU (18)

TSOKACINMU NA YAU (18)

March 18, 2025
TSOKACINMU NA YAU (11)

TSOKACINMU NA YAU (11)

March 11, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)
  • General Buratai (A Poem)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

April 27, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.