• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, January 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

SAƘON ADDU’A DA TAYA MURNA GA SHUGABAN JAMI’AR FUDMA: FARFESA AMINU ADO KAFUR

SAƘON FATAN ALHERI

Sani Ahmed Malumfashi by Sani Ahmed Malumfashi
May 19, 2025
in Gizago
0
SAƘON ADDU’A DA TAYA MURNA GA SHUGABAN JAMI’AR FUDMA: FARFESA AMINU ADO KAFUR
30
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

SAƘON ADDU’A DA TAYA MURNA GA SHUGABAN JAMI’AR FUDMA: FARFESA AMINU ADO KAFUR

Daga Sani Ahmed Malumfashi

Related posts

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)

January 13, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (7)

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (7)

January 9, 2026
Shugaban Jami’ar FUDMA, Farfesa Aminu Ado Ƙafur, a gefe kuma Sani Ahmed Malumfashi

 

                          __________

Ni Sani Ahmed Malumfashi da dukkan iyalai da ‘yan uwa da abokan arziki, muna miƙa saƙon addu’a da taya murna ga mai girma Shugaban Jami’ar Gwamnatin Tarayya Dutsin-ma, Jihar Katsina, Farfesa Aminu Ado Ƙafur.

Wannan babban matsayi da shugabanci da ka samu, ya nuna ƙarara irin jajircewarka, hangen nesa, da kuma kishinka wajen ciyar da harkar ilimi gaba a Najeriya.

Zaɓen ka ba abin mamaki ba ne ga duk wanda ya san ka, ko kuma yi aiki tare da kai. Ka daɗe kana nuna ƙwarewa a harkar shugabanci, gaskiya da riƙon amana, da kuma jajircewa wajen ganin an cin ma nasara a dukkan al’amura. Halayenka na tausayi, adalci da kuma ƙwarewa sun sa kowa yake girmama ka, ya kuma koyi abubuwa masu amfani a ƙarƙashin jagorancinka.

A matsayinka na shugaba, kana jagoranci da haƙuri da hangen nesa, kana kuma ƙarfafa gwiwar ma’aikata da abokan aiki. Ka kafa kyakkyawan tarihi na iya mu’amala da kowa, kana sauraron kowa, kana kuma ba kowa dama ya nuna ƙwarewarsa. Waɗannan halaye naka na musamman, za su taimaka matuƙa a sabon matsayin da Allah ya ɗora maka.

A baya, ka sha nuna ƙwarewa wajen haɗa kan jama’a da kawo cigaba. Muna da yaƙinin cewa, Jami’ar FUDMA za ta ƙara haɓaka da bunƙasa a ƙarƙashin jagorancinka, ta fuskar ingancin karatu, bincike, da kuma rawar da jami’ar ke takawa a ci gaban ƙasa. Salon shugabancinka mai cike da tawali’u da hangen nesa ne – daidai abin da ake buƙata a wannan lokaci.

Wannnan sabon matsayi da Allah ya ba ka, yana ɗauke da manyan nauye-nauye da ƙalubale iri-iri, amma muna da tabbacin cewa za ka shawo kansu da ƙwarewa da kwarjini tare da taimakon Allah. Ƙwarewarka, nutsuwarka, da kuma adalcinka za su taimaka matuƙa wajen tafiyar da al’amuran jami’ar cikin kwanciyar hankali da ci gaba.

Mu, a matsayinmu na yaranka, waɗanda muka amfana da shiriya da jagorancinka, muna alfahari da wannan babban ci gaba da ka samu. Wannan nasara ba taka kaɗai ba ce – ta dukkanmu ce. Muna fatan Allah ya ƙara ɗaukaka ka, kuma ya ba ka nasara a dukkan matakan rayuwa.

Yayin da kake fara wannan sabon babi na rayuwarka, muna roƙon Allah ya ƙara maka basira da lafiyar jiki da ta zuciya. Allah Ya ba ka ikon sauke nauyin da aka ɗora maka cikin nasara. Muna fatan alheri da ganin nasarori masu tarin yawa a lokacin mulkinka a matsayin Shugaban Jami’a Federal University Dutsin-ma.

Wasallam.

Naka da ladabi da biyayya,

Sani Ahmed Malumfashi

Previous Post

CONGRATULATIONS TO ESTEEMED VC FUDMA: PROF. AMINU ADO KAFUR

Next Post

Nazari Da Sharhin Littafin “Sai An Yi Da Gaske”

Related Posts

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)
Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)

January 13, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (7)
Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (7)

January 9, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (6)
Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (6)

January 6, 2026
Next Post
Nazari Da Sharhin Littafin “Sai An Yi Da Gaske”

Nazari Da Sharhin Littafin "Sai An Yi Da Gaske"

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

KTSTA: HARKAR SUFURI A HANNUN GWANI (1)

KTSTA: HARKAR SUFURI A HANNUN GWANI (1)

July 9, 2025
Humility and Gentility: My Encounter with Dr. Bukar Usman

ZIYARA GA BUKAR USMAN: Ganawa Da Mutum Mai Karimci Da Tawali’u

October 19, 2023
Gizagawa Sun Yi Rashi A Katsina

Gizagawa Sun Yi Rashi A Katsina

July 13, 2023
My Takeaways from IBB’s Autobiography

My Takeaways from IBB’s Autobiography

March 18, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation
  • Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
  • Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.