• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, April 26, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

AMBALIYA

WAKEN FASAHA

Khalid Imam by Khalid Imam
September 11, 2024
in Adabi
0
AMBALIYA

Ambaliya

25
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

AMBALIYA

Daga Khalid Imam

Related posts

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026

°°°°°°°
A daminar bana, Allah Ya jarabci sassan Najeriya da ambaliya, inda a makon nan ruwa ya mamaye kusan dukkan birnin Maiduguri. An yi asarar dukiya da ta rayuka. Khalid Imam ya rubuta wannan waƙe, domin jajantawa.
°°°°°°°

Ambaliya

Dubi dai ambaliyar, nan,
Ta share Shira da Buji,
Gwaram da Gadau Katagum
Je Buskuri ɗan uwana.
Yau ba hanya ta mota,
Ruwa duka ya malale.

Dorina ga naki cinye,
Ko’ina ka bi babu hanya,
Gonakin da yawan mutane,
Gidaje kasuwanni,
Ruwa ya lamushe su,
Masu mulki ba ruwansu.

Ruwa yau ya ci Borno,
Har fadar Shehu namu,
Ruwan ambaliya yau,
Bai bar Zazzau ba can ma,
Wasu ma sassan Kano yau,
Ruwa duka ya malale.

A ƙasa in shugabanni,
Gwamnoni masu mulki,
Sata ce alƙiblarsu,
Don takaici cin amana,
Sai su bar lamarin mutane,
Su yi ta harkokin gabansu.

Da suna da kula da gaske,
Da suna kishin jiharsu,
Da ba su barin mutane,
A halin ha’ula’i,
Ruwa ya kai su bango,
Ya shaƙe kwalar wuyansu.

Sakaci ne ko mugunta,
Zai sa gwamna ya manta,
Cewa jama’ar jiharsa,
Ruwa na hallaka su,
Ya ƙi yin komai da kansa,
Tun da ba zaɓe ake ba.

Tun da ba zaɓe a gobe,
Da zai zo yai ta kamfen,
Ya yi ƙarya don a zaɓar,
Ai ta ma ambaliyar man,
Masu yin zaɓe ta shafa,
Shi yana ofis a zaune.

Dukiyar jama’ar jiharsa,
Ta amana bai kula ba,
Shi da sauran masu mulki,
Suna wawa a kullum,
Lamarin jama’a ko oho,
Wannan ai su ta shafa.

Don sun iya cin amana,
Shugaba na ƙasa yana ji,
An sanar masa shi da gwamna,
Cewa bana babu shakka,
Sauyin yanayi da gaske,
Tarko yai wa mutane.
_______________
© Khalid Imam
Satumba, 2024

Previous Post

LAMENTATION FOR MAIDUGURI

Next Post

Dr. Bukar Usman Floods German Universities with his Books:

Related Posts

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza
Adabi

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)
Adabi

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
Let’s Speak Our Mother Tongue
Adabi

Mu Yi Kishi Da Alfahari Da Harshen Uwa

March 6, 2026
Next Post
Dr. Bukar Usman Floods German Universities with his Books:

Dr. Bukar Usman Floods German Universities with his Books:

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

RAMADAN KARIM: 30-1447

RAMADAN KARIM: 30-1447

March 19, 2026
An Kama Wasu Mata Da Ke Safarar Makamai Zuwa Katsina

An Kama Wasu Mata Da Ke Safarar Makamai Zuwa Katsina

October 2, 2023

December 5, 2023
KISAN MAWAƘI MOHBAD: Darasi Da Jan Hankali G Al’ummar Arewa

KISAN MAWAƘI MOHBAD: Darasi Da Jan Hankali G Al’ummar Arewa

September 22, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Duniya Ba Gidan Zama Ba
  • Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi
  • Governor Dikko Radda Commissions Community Development Projects Built by Muntari Sagir in Malumfashi

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Duniya Ba Gidan Zama Ba

Duniya Ba Gidan Zama Ba

April 24, 2026
Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

April 22, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.