SHARI’AR MUSULUNCI: Bayan Yaƙi Da Baɗala, A Yaƙi Ɓarayin Gwamnati, Hanci Da Rashawa
~~~~~~~
Ra’ayi Daga Abdullahi Dahiru
~~~~~~~
A shekarar 1999, Gwamnan Zamfara na lokacin, Ahmad Sani Yeriman Bakura ya yi shelar ƙaddamar da Shari’ar Musulunci a jiharsa. Aka yi gagarumin taron ƙaddamarwa.
Ba a daɗe ba abin ya zama kamar wutar daji. Sauran jihohin Arewa masu rinjayen musulmi, su ma suka ƙaddamar.
Bayan ƙaddamarwar, aka ce duk waɗansu dokokin addinin Musulunci za a ɗabbaƙa su, ba wadda ba za a yi ba. Aka sha riciki da Gwamnatin Tarayya da al’ummar da ba musulmi ba saboda nuna adawar su da ƙaddamar da shariar.
Musulmi sun goyi bayan ƙaddamar da shari’ar ce da fatan cewa za a yi adalci sannan rayuwarsu za ta inganta. Amma sai su masu gudanar da ita shari’ar suka mai da hankali kan hukunce-hukuncen da suka shafi laifuffuka kamar shan giya da zina da sata. Suka nuna kamar su ne kaɗai shari’a; in an tsaida su za a yarda ana Shari’ar Musulunci.
Amma ba su maida hankali wajen riƙe amanar dukiyar mutane da yi musu ayyukan da za su kawo ci gaban al’umma ba, kamar bunƙasa ilmi, lafiya da sauransu.
Sai ya zama a waɗannan jihohi babu abin da ya canza wajen harkar tafiyar da gwamnati. Aka ci gaba da cin hanci da rashawa da satar kuɗin al’umma, babu wani hukunci.
A Zamfara aka kama wani mai suna Bello Jangeɓe da laifin sata, aka zartar masa da hukuncin yanke hannu kuma aka yanke hannun. Amma in an ƙalubalanci wadannan gwamnatocin cewa, me ya hana hukunta ɓarayin gwamnati? Sai su ce ai su cin amana suka yi ba sata ba, babu hukuncin haddi a kansu.
Aka kafa hukumomin hisba a waɗannan jihohin don su tabbatar da bin dokokin shari’a.
A dai Jihar Zamfara, an samu mata da aka samu sun haihu bayan aurensu ya mutu da daɗewa, aka yi musu zargin zina. Kotuna suka yanke musu hukuncin rajamu. Sai da suka ɗaukaka ƙara aka soke hukuncin. Hisba suna bi gidajen giya da mata suna kame suna farfasa giya.
Haka aka ci gaba har wannan lokacin. Amma bayan irin ayyukan yaƙi da sai da giya da kamen mata masu zaman kansu, akwai sauran hukuncin shari’ar da ake ɗabbaƙawa?
Su kansu hukunce-hukuncen, kamar an ware waɗansu al’umma ne ake hukunta su kuma a ƙyale masu galihu da manya, idan sun yi irin waɗannan laifuffukan.
Misali, a Jihar Kano an sami bidiyo na wani shugaba yana saka Daloli a aljihu. Ga maganganu ana yi na kwangilolin tituna har da kana sunayen titunan da unguwannin da suke. Inda ake shari’a ta Allah, lallai ya kamata a bincika wannan zargi, koda shugaban yana da kariya a Shari’ar Bature. Aƙalla a kira shi a tuhume shi, cewa kudin mene ne?
Wataƙila a saka shi ya rantse cewa kuɗin nan ba satar su ya yi ba, nasa ne na halal. Shin an yi haka?
Kuma wannan gaba ɗaya al’ummar ce ba da gaske take yi wajen neman adalci ba.
Hisba tana kamen giya ta farfasa. In ka duba a cikin Musulmi ɗari, nawa suke shan giya? Wataƙila ka sami mutum biyar. Masu shan ƙwaya da wiwi fa? Za ka same su da yawa. Me ya sa aka mai da hankali kan giya ita kaɗai, aka ƙyale sauran kayan maye? Ka ga dole waɗanda ake ƙwace wa giyar, waɗanda yawanci ba musulmi ba ne, su yi zargin su kaɗai aka ware ake aiwatar da hukunci a kansu. Bayan kuma an ce shari’a ba za ta shafe su ba.
Yaran da ake kamawa da zargin yawon banza, in ka duba yawanci wani hali ne na rayuwa da rashin galihu ya jefa su haka. Kuma ana kamen karuwai, fyaɗe da jarirai da ake haifa ba iyaye suna ƙaruwa a cikin lunguna. Maimakon a nemi hanyar fid da su daga wannan halin sai a kira ‘yan jarida ana holin su. Abin ya zama kamar cin zarafi maimakon neman gyaruwar waɗanda aka kama ɗin.
Su kuma jagorori, ‘ya’yansu suna makarantu ko a ƙasashen waje ko na gida, ba yadda za su shiga waɗannan matsalolin.
Akwai lokacin da za ka ga an kama samari an yi musu aski saboda sun tara gashi na rashin tarbiyya. Amma kuma ga ‘yan ƙwallo da ‘yan fim suna da irin wannan gashin ko wanda ya fi shi muni, ana kallon su amma ba a yi musu komai ba.
Mutane sun ga me ya faru a lokacin bikin ‘yar gwamna da ya wuce. An ɗauka Hisba za su kai ɗauki, ba su kai ba. Ko da ba su kai ba, lokacin za su iya gayyatar mutanen, su tuhume su yadda suke yi wa sauran mutane. Amma uzurin da suke bayarwa shi ne, abin ya fi ƙarfinsu kuma tun da suna ɗabbaƙa shari’a kan talakawa, ba dole su ɗabbaƙa kan shugabanni ba.
Ga jihohin da ake shari’ar, irin su Zamfara suna fama da matsalolin garkuwa da mutane da hare-haren ‘yan bindiga. Kuma an ga yadda gwamnatocinsu suke wabdaƙa da kuɗaɗen al’umma kuma sun kasa warware waɗannan matsaloli.
Waɗansu matsalolin maganinsu ma shi ne ba da ilmi da rage talauci da riƙe amanar dukiyar al’umma. Shin shugabannin suna yin haka?
Da yawa in mun yi irin waɗannan maganganu, ana yi mana zargin munafunci. Amma maganar gaskiya akwai gyara, yadda ake tafiyar da Shari’ar Musulunci a Arewacin Najeriya.
~~~~~~~
Dokta Abdullahi Dahiru, ƙwararren likita ne kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum.
~~~~~~~













