Muhimman Ayyukan Da Shugaba Tinubu Ya Ɗora Mani – Ministan Yaɗa Labarai
Daga Wakilinmu
~~~~~~~
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ɗora masa nauyin jaddada tasirin kishin ƙasa, aiki da gaskiya da kuma kawar da nuƙu-nuƙu, a matsayin kyawawan ɗabi’un da gwamnatin sa za ta ɗore kan turbarsu.
Ministan ya bayyana haka a cikin tattaunawar da ya yi da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), a Abuja.
Ya ce ajandar Fata Nagari Lamiri da Gwamnatin Shugaba Tinubu ta hau mulki da ita, wani kyakkyawan muradi ne na ɗaukaka Nijeriya zuwa ƙololuwar nasara da bunƙasa a cikin manyan ƙasashe na duniya, tare da goge baƙin fentin da ake kallo a jikin wannan ƙasa.
Idris ya ce Tinubu ya hore shi da cewa ya tabbatar ya samu nasarar wayar da kan ‘yan Nijeriya cikin shekaru kaɗan masu zuwa, ta yadda aƙalla za a iya sake kankaro ƙima da martabar ƙasar nan, tare da fara ɗora ta bisa kyakkyawar turbar da ta fi dacewa ta bi.
“Wannan kuwa babban kalubale ne. Saboda kun dai san ba a zukatan matasa kaɗai ɗa’a da kishi suka yi ƙaranci ba, har ma a zukatan yara da manya.
“Ina ganin dalili ke nan shugaban ya canja wa sunan Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Bunƙasa Al’adu, zuwa Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai.
“Hakan ke nan yana nufin Shugaban Ƙasa na so a ɗora batun wayar da kai da cusa kishin ƙasa a sahun gaba,” cewar Idris.
Ministan ya ƙara da cewa tasirin kishin ƙasa da aiki da gaskiya da Tinubu ke ta faɗi-tashin cusawa da kwaɗaitarwa.
“Ya ba mu umarnin kai-tsaye cewa mu tabbatar waɗannan kyawawan ɗabi’u da halaye nagari sun kasance jigo a ƙoƙarin faɗakar da akasarin ‘yan Nijeriya.”
~~~~~~~












