• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, March 8, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Addini

Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Tumbu-Madalla

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
July 21, 2023
in Addini
0
Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Tumbu-Madalla

Muharram, 1445 Hijriyya

20
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Tumbu-Madalla

A yau Juma’a, 03-01-1445 (Hijriyya) = 21-07-2023 (Miladiyya), Limamin Masallacin Unguwar Tumbu da ke Garin Madallah, Ƙaramar Hukumar Tafa, Jihar Neja ya gabatar da huɗubar mai taken Muhimmancin Watan Muharram.

Related posts

RAMADAN KARIM: 19-1447

RAMADAN KARIM: 19-1447

March 8, 2026
RAMADAN KARIM: 18-1447

RAMADAN KARIM: 18-1447

March 7, 2026

Liman ya buɗe huɗubarsa da godiya ga Allah da salati da sallama ga Manzon Allah, Muhammadu (saw). Ya buƙaci al’umma da mu ji tsoron Allah a kowane lokaci. “Mu jajirce wajen roƙon Allah, domin Ya sahale mana shiriya, domin yi masa ɗa’a da jin tsoron Sa a kowane lokaci,” in ji Liman.

Ya bayyana mana cewa, Allah Ya halicci rayuwa da mutuwa ne domin jarabawa ga bayinSa, don tantance wanda ya fi aiki mai kyau. Saboda haka mu dage wajen aikata kyawawan ayyuka, mu guje wa munana iya gujewa, domin mu rabauta a ranar lahira.

Liman ya ce lallai watan Muharram yana da girma da matsayi na musamman a cikin watannin Musulunci. Domin kuwa yana cikin watanni huɗu masu alfarma – Zulƙida, Zulhijja, Muharram da Rajab. Haka kuma shi ne wata na farko a jerin watannin Musulunci.

A cikin Muharram, akwai rana ta musamman, ta 10 ga wata, wacce take da muhimmanci, kasancewar a ranar ce Allah (swt) Ya kuɓutar da Annabi Musa (as) da mutanensa, Ya halaka Fir’auna da mabiyansa a cikin teku.

Liman ya kawo sahihan hadisai daga Manzon Allah (saw), cewa Musulmi su azumci wannan rana ta 10 ga Muharram. Haka kuma a haɗa da ranar 9 ga wata, domin saɓa wa Yahudawa da Nasara. Ke nan azumin biyu za su kama ranakun Alhamis da Juma’a masu zuwa ke nan in Allah Ya yarda.

Malam ya bayyana irin falalar da ke akwai ga wanda ya azumci Tasu’a da Ashura, cewa Allah zai kankare zunubban bawa na shekarar da ta gabata.

Liman ya yi gargadi ga al’umma da mu nisanci bidi’o’in da aka ƙirƙiro game da watan Muharram, kamar shafa kwalli sau bakwai, yin ado ko wata salla ta musamman a ranar 10 ga wata, ko yin abincin cika-ciki da kuma yin hasashen abin da zai faru a shekarar da sauransu.

Malam Ya rufe huɗubarsa da addu’a ta musamman ga al’umma. Alheran da ke cikin shekarar, Allah Ya datar da mu da su, Ya kiyaye mu daga sharruka da fitintinun da ke cikinta.

Amin summa Amin.

Previous Post

Mutane Sun Koma Tafiya Ƙasa A Abuja

Next Post

NASIHA: Waƙen Ƙarfafa Gwiwa

Related Posts

RAMADAN KARIM: 19-1447
Addini

RAMADAN KARIM: 19-1447

March 8, 2026
RAMADAN KARIM: 18-1447
Addini

RAMADAN KARIM: 18-1447

March 7, 2026
RAMADAN KARIM: 17-1447
Addini

RAMADAN KARIM: 17-1447

March 6, 2026
Next Post
NASIHA: Waƙen Ƙarfafa Gwiwa

NASIHA: Waƙen Ƙarfafa Gwiwa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
KADA Honours Ambassador A. Y Shehu with Excellent Award

KADA Honours Ambassador A. Y Shehu with Excellent Award

September 1, 2024
Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

January 4, 2026
Hassan Maina Kaina Ya Zama Babban Editan Africa Radio International Na Farko

Hassan Maina Kaina Ya Zama Babban Editan Africa Radio International Na Farko

October 9, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • RAMADAN KARIM: 19-1447
  • FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)
  • RAMADAN KARIM: 18-1447

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

RAMADAN KARIM: 19-1447

RAMADAN KARIM: 19-1447

March 8, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.