Daga Hamadani Buba
Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma
Wata Alhajiya da ke Aikin Hajjin bana a ƙasa mai tsarki, Saudiyya, ta tsinci Dalar Amurka Dubu 80, kimanin Naira Miliyan 60 a kuɗin Najeriya kuma ta miƙa su ga hukuma domin a yi cigiyar mai su, kamar yadda Cibiyar Kula Da Alhazai ta Jihar Sakkwato ta bayyana.
Matar mai suna Hajiya A’ishatu ‘Yanguru Nahuche, asalin daga Zamfara take. Bayan ta tsinci waɗanan maƙudan kuɗi, ba ta ɓata lokaci ba ta miƙa su ga Hukumar Alhazai ta Jihar jihar Zamfara, domin cigiyar masu kuɗin.
Da yake yaba wa halayyar Hajiya A’ishatu, ƙwararren ɗan jarida, Sakataren Watsa Labarai na Shugaban Jam’iyyar PDP na Ƙasa, Alhaji Yusuf Dingyaɗi ya ce: Haƙiƙa wannan ba ƙaramar karramawa da shaidar ƙwarai ta samu ba, mussaman kasancewar ta mutunniyar kirki da ke tsoron Allah da kwaɗayin rahamar Allah. Allah Ya saka mata da alheri.”













Masha allah
Alhamdu lillah. Allah biya.
Amin Amin. Muna godiya sosai.