Daga Abdullahi Ibrahim Mahuta
University of Health Sciences Funtuwa/Malumfashi: Ƙarin Haske A Kan Lamarin (2)
Kamar yadda na yi bayani a baya, bayan da Shugaban Majalisar Dattawa ya samu Shugaban Ƙasa a kan wannan shiri na majalisa na ƙirƙiro waɗannan jami’o’i, maganar ta koma a hannun ɓangaren executive. Wannan ya faru a shekarar 2022 ke nan. Wannan ganawa kuma ita ta kawo ƙarshen duk wani shiri da ɓangaren majalisar take yi na ganin an ƙirƙiro waɗannan jami’o’i ta hanyar ƙudiri na majalisa.
Amma shekara ɗaya bayan nan, a cikin wata takarda da ta fito daga Ofishin Ministan Ilimi zuwa Ofishin Shugaban Ƙasa kasa ta hannun Chief of Staff na Shugaban Ƙasa, takardar ta yi bayani kamar haka:
“A cikin Kundin Tsare-Tsare na Gwamnatin Tarayya A Kan Harkar Ilimi wanda za ta gudanar daga 2018 -2023. Gwamnatin ta yi ƙudirin kafa waɗansu jami’o’i guda uku a kowane zone na ƙasar nan. Waɗannan jami’o’i kuma su ne kamar haka.
1. University of Medical Health Sciences
2. University of Technology
3. University of Agriculture.
Takardar ta ci gaba da cewa a zuwa yanzu, Gwamnatin Tarayya tarayya ta kafa waɗannan jami’o’i na Medical Sciences a zones guda huɗu na ƙasar nan kamar haka:
1.. Otukpo, Benue State(NC)
2. Azare, Bauchi State (NE)
3. Ila Oragun, Osun State (SW)
4. Abakaliki, Ebonyi State (SE)
Takardar ta ci gaba da bayanin cewa tana neman umurnin Shugaban Ƙasa domin kafa sauran biyu da suka rage kamar haka:
1. University of Medical Sciences Katsina, katsina State (NW)
2. University of Medical Sciences Kwale, Delta State (SS)
A haka Kuma Shugaban Ƙasa ya ba da approval. Wanda kuma tuni har an fara naɗe-naɗen shugabannin waɗannan sababbin jami’o’i.
To ganin wannan sabon shirin na Gwamnatin Tarayyar, na kai wannan sabuwar jami’a zuwa garin katsina, shi ya sanya su waɗannan dattawa na garin Funtuwa suka nemi ganawa da mai girma Gwamna, inda suka gabatar masa da roƙon ya taimaka ya sa baki a dawo da wannan jami’a zuwa garin Funtuwa, inda nan ne headquarter ta Funtuwa Zone.
Wannan buƙata kuma, ita ce mai girma Gwamna ya amsa masu. Inda ya yi ƙarin bayani da cewa ko da ba su zo ba, to dama yana da niyyar aikata hakan, ganin cewa yankin Katsina akwai jami’o’i har guda uku.
Wannan shi ne sakamakon ƙarin bincike da na gudanar. Abin da ban sani ba shi ne list ɗin da Shugaban Majalisar ya miƙa ma Shugaban Ƙasa, wanda ke ɗauke da sunan Malumfashi, shi ne Ma’aikatar Ilimi ta yi amfani da shi ta canza locations ɗin ko kuma dama can ita Gwamnatin Tarayya tana da nata list ɗin?
Amma dai abin da ya tabbata shi ne ba Jami’ar Malumfashi ba ce mutanen Funtuwa suka je ƙwacewa. Abin da ya jawo wannan rashin fahimta shi ne communication gab da aka samu tsakanin juna, musamman kuma da yake mutane suna da sanin cewa akwai labarin wannan jami’a da Senate suka yi proposing a Malumfashi.
Daga ƙarshe, ina mai ba da haƙuri ga waɗannan dattawa na Funtuwa da kuma ɗaukacin jama’ar wannan yanki, a kan munana zato da mutanenmu suka yi a kan wannan al’amarin, a bisa dalilin ƙarancin bincike
I’m really very sorry! A yi haƙuri da ajizancin ɗan Adam!












