Daga Bashir Yahuza Malumfashi
A yau Juma’a, 19-12-1444 (Hijriyya) = 07-07-2023, Limamin Masallacin Unguwar Tumbu da ke garin Madalla, Ƙaramar Hukumar Tafa, Jihar Neja, ya gabatar da huɗuba, wacce maudu’inta ya kasance “Muhimmancin Sallar Juma’a A Musulunci.”
Bayan gabatarwa, girmamawa da yabo ga Allah (swt) da sallama da salati ga fiyayyen talikai, Manzon Allah, Muhammadu (saw), Liman ya jawo hankalin al’umma da mu ji tsoron Allah, mu riƙe Musulunci da gaske. Ya ce mu sani fa Allah Ya cika mana addininmu, wanda shi ne babbar ni’imar da babu kamar ta a bayan ƙasa.
Ya bayyana mana cewa Allah Ya farlanta mana rukunonin addini guda biyar, ciki kuwa har da salloli biyar a rana, ciki kuwa har da Sallar Juma’a.
Kamar yadda Liman ya nusar da mu, yana daga falalar Sallar Juma’a mutum ya yi gaggawar zuwa masallaci, domin samun babban rabo. Kada mutum ya sake wani abu ya shagaltar da shi daga halartar Sallar Juma’a.
Liman ya nusar da mu wasu daga ladubban Jumu’a – mutum ya yi wanka, ya yi alwala, ya saka sutura mai kyau da turare mai ƙanshi. Mutum ya yi nafilfili, ya yi salati mai yawa ga Manzon Allah (saw). Mutum ya natsu ya saurari huduba, kada ya yi magana da kowa.
Liman ya sanar da mu wani hadisi na Manzon Allah, wanda ke cewa babu Jumu’a ga duk wanda ya yi magana a yayin huɗubar Jumu’a.
Haka kuma ya sake kwaɗaitar da al’umma game da falalar Sallar Juma’a, inda ya sanar da mu wani hadisi, inda Manzon Allah (saw) ke cewa, duk wanda ya yi alwala, ya je Sallar Juma’a, ya yi nafila, ya samu huɗuba, to an yafe masa zunubbansa na makon, har ma da ƙarin kwana uku gaba.
Liman ya tsoratar da mu ga barin Sallar Juma’a. Ya kafa mana shaida da hadisin Manzon Allah (saw), cewa duk wanda ya yi fashin Sallar Jumu’a sau uku a jere, ba tare da wani uzuri amsasshe ga Shari’a ba, to an rufe zuciyarsa.
Wanda kuwa ya bari Allah Ya rufe masa zuciya, tabbas ya taɓe. Allah Ya kiyashe mu, Amin.
Malam Ya ja hankalinmu da mu guji yin duk wata hulɗa ta kasuwanci ko aiki a daidai lokacin Sallar Jumu’a, domin kuwa haramun ne. Amma babu laifi mutum ya koma bakin aikinsa ko sana’a, da zarar an kammala Sallar Jumu’a.
Malam ya rufe huɗubarsa da kyakkyawar addu’a ga al’ummar ƙasa. Allah Ya sa mu dace da rahamarSa, Ya ba mu lafiya da zaman lafiya da imani da yalwar arziki. Amin.













