Daga

Bashir Yahuza Malumfashi
A ranar Lahadin da ta gabata, Dakarun Sojojin Bataliya ta 5 suka kai samame karkarar Azuzuama da ke Ƙaramar Hukumar Ijaw ta Kudu, Jihar Bayelsa; inda suka yi nasarar ƙwato muggan makamai daga hannun bijirarrun ɓarayin ɗanyen mai.
A yayin samamen, ɓarayin sun gamu da gamonsu, inda dakarun sojan suka farmake su, suka gudu suka bar maɓoyar tasu kuma suka bar muggan makamansu a warwatse.
Dakarun sun yi nasarar ƙwato bindigogi 5 ƙirar AK 47, Rokket ta jefa gurneti guda 2 da Rokket ta jefa bamabamai guda 4 da alburusai na musamman masu girman milimita 7.62 da magazin guda 14 na AK 47 da kuma injin zuƙo mai guda ɗaya. Da sauran kayayyakin da suke amfani da su wajen gudanar da haramtattar sana’ar tasu.
Tuni dai dakarun suka lalata maɓoyar tasu, suka balbala mata wuta.
Daraktan Watsa Labarai na Rundunar Sojojin Najeriya, Birgediya-Janar Onyema Nwachukwu, a madadin rundunar ya miƙa godiya ta musamman ga al’ummar yankin, inda ya roƙe su da su ci gaba da ba sojoji haɗin kai, wajen ba su bayanan sirri dangane da muggan iri. Ya ce Rundunar Sojojin Najeriya a shirye take domin yaƙi da ɓatagari a yankin.













