Daga Bashir Yahuza MalumfashiI
~~~
Idan ana maganar noman zamani a Jihar Jigawa, sunan Alhaji Isa Billami Haɗeja yana sahun gaba. Taskar Gizago ta tattauna da shi, inda ya yi bayanin yadda manoma ke tunkarar daminar bana. Ga yadda tattaunawar ta kasance:
~~~
TG: Ko za ka gabatar mana da kanka a taƙaice?
BILLAMI: Ni dai haifaffen garin Haɗeja ne na Jihar Jigawa. An haife ni shekaru 56 da suka shige. Na yi karatun addini a gidanmu da na zamani kuma na yi aikin Gwamnati haɗe da kasuwanci da noma da kuma kiwo.
TG: Yaya gonarka ke shirin noman bana?
BILLAMI: Alhamdu lillah. Kamar kowace shekara, a bana mun sake duƙufa wajen noman damina, musamman gero, dawa, wake, riɗi, zoɓo da kuma gyaɗa. Abin da ya sa muka sauya akalar ba da muhimmanci a kan abubuwan da na lasafta a sama shi ne yawan hasarar da muke samu a noman shinkafa, sakamakon ambaliya da muke fuskanta duk shekara a gaɓar Kogin Haɗeja da sauran fadamu da ke yankunanmu. Don haka muka juya akalarmu zuwa noman tudu, na damina ke nan. Kuma alhamdu lillah, muna samu sosai.
TG: Yaya batun noman rani da ya gabata, waɗanne nasarori ko akasi aka samu?
BILLAMI: A gaskiya noman rani a ƙasar Haɗeja ya samu tasgaro mai yawan gaske a ‘yan shekarun nan, kasancewar ambaliyar ruwan kogi da muke fuskanta rani da damina. A gefe ɗaya kuma ga tsadar kayayyakin sinadarai da kayan noma, kamar su taki, iri, maganin feshi da na ƙwari da tsadar ƙwadagon ‘yan aiki. Amma duk da haka ƙalilan da suke da hali sun daure sun aikata, sai dai abin takaicin shi ne a wasu wuraren a tun halin yanzu ruwan sama bai kankama ba amma ambaliya ta shanye mafi yawa daga gonakin al’umma.
Wannan barazanar ta ambaliya da muke fuskanta rani da damina, ta kassara manoma da dama a wannan yanki na Haɗeja. Bayan haka akwai wasu nau’in abubuwa da suke kama da ambaliyar, suma suna taka rawa wajen durƙusar da noma da manoma a wannan yankin.
Abubuwan da suka durƙusar da manoma kuwa su ne kamar haka: Ambaliya, Kwarona, Canjin Kuɗi, Ɓarnar Makiyaya, Satar Kayan Aiki, kamar injin banruwa da kuma satar amfanin gona tun yana tsaye a gonar, ba a yanke ba. Sai kuma tsadar Kuɗin Ƙwadago.
Waɗannan abubuwan da na lissafta, su suka kawo tasgaro wajen ci gaban noma a wannan yanki.
Ɓangaren ci gaba kuma a gaskiya kafin waɗancan matsaloli da na lissafta a baya, manoma suna cikin walwala, domin a eka ɗaya muna girbar shinkafa kamar buhu 50 zuwa 55 a kowace eka.
TG: Yaya batun sabuwar gwamnati da noma, ko akwai shawarwarin da za ka ba Gwamnan Jihar Jigawa dangane da noma da kiwo?
BILLAMI: Shawarwarina ga gwamnati su ne: Na farko dai a magance matsalar ambaliya. Na biyu a samar da ƙaƙƙarfan kwamiti domin magance rikicin manoma da makiyaya. Na uku, a samar da ingantattun iri da kayan feshi da maganin ƙwari da samar da ƙwararrun malaman gona, domin Ilimantar da manoma a kan dabarun noman zamani. A ɗaya ɓangaren akwai buƙatar Gwamnati ta kalli sauran ɓangarorin noma, kamar kiwon kaji da kifi da dabbobin nama da noman itatuwa, kamar mangwaro da dabino da lemo da ayaba da abarba da zogale da makamantansu.
TG: Ko akwai wani ƙarin bayani da za ka ƙara, wanda ban tambaye ka ba?
BILLAMI: Kasancewar Gwaman Malam Umar Namadi (Ɗanmoɗi) manomi ne, ina kira a gare shi da ya bai wa fannin noma, kiwo da Kasuwanci muhimmancin gaske. Domin noma sh ine ginshiƙi, kuma ƙashin bayan tattalin arzikin kowace nahiya da al’umma. Muna yi masa fatan ya zaƙulo zakakuran mutane, bisa ƙwarewa da cancanta, ya sanya su musamman a fannin noma da kiwo.
















Nice