• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, January 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Noma Da Kiwo

Ambaliya Ce Babbar Ƙalubalen Manoman Jigawa – Isa Billami

Akwai Bukatar Gwamnati Ta Tallafa

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
June 12, 2023
in Dausayin Kauna
1
Ambaliya Ce Babbar Ƙalubalen Manoman Jigawa – Isa Billami

Alhaji Isa Billami a gonarsa

137
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Daga Bashir Yahuza MalumfashiI

~~~

Related posts

Shin Wai Akwai So? (1)

Shin Wai Akwai So? (1)

June 5, 2025
MENE NE SO?

MENE NE SO?

April 27, 2025

Idan ana maganar noman zamani a Jihar Jigawa, sunan Alhaji Isa Billami Haɗeja yana sahun gaba. Taskar Gizago ta tattauna da shi, inda ya yi bayanin yadda manoma ke tunkarar daminar bana. Ga yadda tattaunawar ta kasance:

~~~
TG: Ko za ka gabatar mana da kanka a taƙaice?

BILLAMI: Ni dai haifaffen garin Haɗeja ne na Jihar Jigawa. An haife ni shekaru 56 da suka shige. Na yi karatun addini a gidanmu da na zamani kuma na yi aikin Gwamnati haɗe da kasuwanci da noma da kuma kiwo.

TG: Yaya gonarka ke shirin noman bana?

BILLAMI: Alhamdu lillah. Kamar kowace shekara, a bana mun sake duƙufa wajen noman damina, musamman gero, dawa, wake, riɗi, zoɓo da kuma gyaɗa. Abin da ya sa muka sauya akalar ba da muhimmanci a kan abubuwan da na lasafta a sama shi ne yawan hasarar da muke samu a noman shinkafa, sakamakon ambaliya da muke fuskanta duk shekara a gaɓar Kogin Haɗeja da sauran fadamu da ke yankunanmu. Don haka muka juya akalarmu zuwa noman tudu, na damina ke nan. Kuma alhamdu lillah, muna samu sosai.

TG: Yaya batun noman rani da ya gabata, waɗanne nasarori ko akasi aka samu?

BILLAMI: A gaskiya noman rani a ƙasar Haɗeja ya samu tasgaro mai yawan gaske a ‘yan shekarun nan, kasancewar ambaliyar ruwan kogi da muke fuskanta rani da damina. A gefe ɗaya kuma ga tsadar kayayyakin sinadarai da kayan noma, kamar su taki, iri, maganin feshi da na ƙwari da tsadar ƙwadagon ‘yan aiki. Amma duk da haka ƙalilan da suke da hali sun daure sun aikata, sai dai abin takaicin shi ne a wasu wuraren a tun halin yanzu ruwan sama bai kankama ba amma ambaliya ta shanye mafi yawa daga gonakin al’umma.
Wannan barazanar ta ambaliya da muke fuskanta rani da damina, ta kassara manoma da dama a wannan yanki na Haɗeja. Bayan haka akwai wasu nau’in abubuwa da suke kama da ambaliyar, suma suna taka rawa wajen durƙusar da noma da manoma a wannan yankin.
Abubuwan da suka durƙusar da manoma kuwa su ne kamar haka: Ambaliya, Kwarona, Canjin Kuɗi, Ɓarnar Makiyaya, Satar Kayan Aiki, kamar injin banruwa da kuma satar amfanin gona tun yana tsaye a gonar, ba a yanke ba. Sai kuma tsadar Kuɗin Ƙwadago.
Waɗannan abubuwan da na lissafta, su suka kawo tasgaro wajen ci gaban noma a wannan yanki.
Ɓangaren ci gaba kuma a gaskiya kafin waɗancan matsaloli da na lissafta a baya, manoma suna cikin walwala, domin a eka ɗaya muna girbar shinkafa kamar buhu 50 zuwa 55 a kowace eka.

TG: Yaya batun sabuwar gwamnati da noma, ko akwai shawarwarin da za ka ba Gwamnan Jihar Jigawa dangane da noma da kiwo?

BILLAMI: Shawarwarina ga gwamnati su ne: Na farko dai a magance matsalar ambaliya. Na biyu a samar da ƙaƙƙarfan kwamiti domin magance rikicin manoma da makiyaya. Na uku, a samar da ingantattun iri da kayan feshi da maganin ƙwari da samar da ƙwararrun malaman gona, domin Ilimantar da manoma a kan dabarun noman zamani. A ɗaya ɓangaren akwai buƙatar Gwamnati ta kalli sauran ɓangarorin noma, kamar kiwon kaji da kifi da dabbobin nama da noman itatuwa, kamar mangwaro da dabino da lemo da ayaba da abarba da zogale da makamantansu.

TG: Ko akwai wani ƙarin bayani da za ka ƙara, wanda ban tambaye ka ba?

BILLAMI: Kasancewar Gwaman Malam Umar Namadi (Ɗanmoɗi) manomi ne, ina kira a gare shi da ya bai wa fannin noma, kiwo da Kasuwanci muhimmancin gaske. Domin noma sh ine ginshiƙi, kuma ƙashin bayan tattalin arzikin kowace nahiya da al’umma. Muna yi masa fatan ya zaƙulo zakakuran mutane, bisa ƙwarewa da cancanta, ya sanya su musamman a fannin noma da kiwo.

Previous Post

Ranar Dimokuraɗiyya: Mu Jajirce Wajen Gina Ƙasa – MD Abubakar

Next Post

Shauƙin Son Faɗakarwa Ya Sa Na Zama Mawaƙi – ABDUL EXTRA

Related Posts

Shin Wai Akwai So? (1)
Dausayin Kauna

Shin Wai Akwai So? (1)

June 5, 2025
MENE NE SO?
Dausayin Kauna

MENE NE SO?

April 27, 2025
KANA SON FAHIMTAR MATA?
Dausayin Kauna

KANA SON FAHIMTAR MATA?

November 9, 2023
Next Post
Shauƙin Son Faɗakarwa Ya Sa Na Zama Mawaƙi – ABDUL EXTRA

Shauƙin Son Faɗakarwa Ya Sa Na Zama Mawaƙi - ABDUL EXTRA

Comments 1

  1. Adamu sale says:
    3 years ago

    Nice

    Reply

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Sojoji Sun Cafke Manyan Dillalan Miyagun Ƙwayoyi

Sojoji Sun Cafke Manyan Dillalan Miyagun Ƙwayoyi

July 19, 2023
Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

June 22, 2023
Nigeria at 64: How Far So Far?

Nigeria at 64: How Far So Far?

October 7, 2024
THE MAN B. Y. M.

THE MAN B. Y. M.

June 28, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation
  • Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
  • Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.