Inna Lillahi Wa’inna Ilaihi Raji’un! Allah Ya Ji Ƙan Malam Lawal

__________
Cikin jimami da alhini na samu labarin rasuwar surukinmu, Malam Lawal Mai Gwanjo, Fadamawa, Malumfashi.
Kamar yadda labari ya same ni, a jiya ne Talata, 23-12-1447 (Hijiriyya)-09-06-2026 (Miladiyya) Malam ya dawo daga sana’arsa a Kasuwar Ƙanƙara, bayan Sallar Magriba. A kan hanya sai ɓarayin daji suka buɗe masu wuta, inda Allah ya amshi rayuwarsa.
A yau Laraba aka gudanar da jana’izarsa bisa tanadin Musulunci.
Ina miƙa saƙon ta’aziyya ga ɗan uwana, Nasir Ibrahim Jume (surukin marigayin), matarsa Jamila (ɗiyar marigayin) da dukkan ‘yan uwa da abokan ariziki da iyalan marigayin.
Muna roƙon Allah ya ji ƙan shi da rahama. Allah ka dube mu da rahama, ka kawo mana ƙarshen wannan ja’iba ta ta’addanci. Amin-Summa-Amin.
__________













