RAMADAN KARIM: 29-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Yau Laraba, Allah ya nuna mana rana ta 29 a Ramadan. Yau ma ga nasiharmu:
‘Yan uwa, muna dai ta yin ban kwana da Ramadan na bana. Bisa ga haka, yana da kyau mu sanya ma zukatanmu babban darasin azumi, watau tsoron Allah. Tsoron Allah shi ne babban ginshiƙin kyakkyawar rayuwa kuma shi ne babban darasin da azumi yake koya mana.
Allah (swt) a cikin Alƙur’aninsa mai girma, a Suratu Hujurat 49:13, yana cewa: “Mafi daraja a wurin Allah shi ne mafi tsoronsa.” Haka kuma a Hadisin Imam Muslim mai lamba 2564, Manzon Allah (saw) ya bayyana cewa “Allah ba ya kallon surarku…”
Tsoron Allah dai ba a sutura ko sura yake ba, yana nan a cikin zuciya. Duk abin da za mu aikata, mu tuna da cewa Allah yana kallonmu, domin idan mu ba mu ganinsa, to shi yana ganinmu kuma zai yi mana hisabi. Ya Allah ka sanya mu cikin bayinka masu biyayya ga shari’arka. Amin-Summa-Amin.
__________













