RAMADAN KARIM: 25-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Yau Asabar, Allah ya nuna mana rana ta 25 a Ramadan. Yau ma ga nasiharmu:
Alhamdu lillah! Godiya ta tabbata ga Allah da ya raya mu zuwa wannan muhimmin lokaci. A yau kuma za mu tunatar da juna ne dangane da muhimmancin sada zumunci. Babu shakka akwai alheri mai yawa a tattare da zumunci. Zumunci yana ƙarfafa zaman lafiya da fahimta tsakanin al’umma.
Allah (swt), a cikin Suratu Muhammad 47:22-23 ya yi gargaɗi mai girma ga al’umma, dangane da yanke zumunci. Manzon tsira, Muhammadu (saw) a Hadisin Bukhari mai lamba 5991 ya ƙarfafa zumunci, ya kuma bayyana babbar ganimar da mai sada zumunci yake samu.
Abin lura dai shi ne, lallai abu ne mai fa’ida a gare mu da mu raya zumunta. Masu hikimar magana sun ce, zumunta a ƙafa take. Allah ya sanya mu zama masu raya zumunci. Amin.
__________













