RAMADAN KARIM: 09-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Bayan haka, a yau Alhamis, Allah ya nuna mana rana ta 9 a Ramadan. Yau ma ga ‘yar nasiha:
A jiya, mun yi nasiha game da gaskiya. A yau kuma za mu taɓo bayani game da ƙarya. A lokacin da gaskiya take alheri a dukkanta, to ita kuma ƙarya sharri ce a gaba ɗayanta. Don haka, muddin muna son alheri da albarka, to mu kiyayi ƙarya da dukkan sabubbanta.
Allah (swt) a cikin Suratul Hajj 22:30, ya gargaɗe mu da cewa: “Ku nisanci maganar ƙarya.” Manzon Allah (saw), a Hadisin Bukhari mai lamba 6094 da Hadisin Muslim mai lamba 607, ya ce: “Ƙarya tana kai wa ga mugunta.”
Ya Allah ka kiyashe mu da ƙarya, ka ƙarfafe mu da gaskiya a dukkan lamurranmu, amin.
__________













