RAMADAN KARIM: 06-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Bayan haka, a yau Allah ya nuna mana rana ta 6 a Ramadan, don haka za mu amfana da juna a wannan rana da ‘yar nasiha:
Nasiharmu ta yau, tana da yanayi iri ɗaya da ta jiya, watau batun mallakar harshe. Lallai ne yana da muhimmanci gare mu, mu riƙa faɗin alheri a kowane lokaci, a mu’amalarmu ta yau da kullum.
Faɗin alheri da guje wa yasassar magana, shi ne tsari da ɗabi’a mai kyau, wanda zai fisshe mu. Hakan zai kare mu daga ɓata wa juna rai kuma zai sabbaba mana zaman lafiya da kwanciyar hankali da juna.
Allah (swt) a Alkur’ani mai girma, Suratu Ƙaf 50:18 yana cewa: “Babu wata magana da yake furtawa face akwai mai rubutawa.”
Haka kuma Manzon Allah (saw) a Hadisin da Bukhari (lamba 6136) da Muslim (lamba 47) suka ruwaito, ya bayyana cewa: “Ya faɗi alheri ko ya yi shiru.”
Wannan ke nuna mana cewa akwai alheri ga mutum ya faɗi alheri a duk lokacin da zai yi magana. Idan kuwa ya san ba alheri zai furta ba, to ya fi masa ya yi gum da bakinsa. Allah sa mu dace, Amin.
__________













