RAMADAN KARIM: 03-1447
__________

Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. ‘Yan uwa, barkanmu da ibadar azumi. Ga shi Allah ya kawo mu rana ta uku a wannan babbar ibada, don haka bari mu yi wa juna nasiha:
Ya ‘yan uwa, lallai ne mu gane kuma mu fahimta da cewa ɗaya daga cikin manufofin azumi shi ne, mu samu halayyar tsoron Allah. Da tsoron Allah ne za mu ji daɗin rayuwar duniya kuma mu rabauta a lahira.
Allah (swt) a cikin Alkur’ani mai girma, Suratun Nahl 16:128 ya ce: “Lalle Allah yana tare da masu tsoronsa.”
Haka kuma Imam Tirmizi, a Hadisi mai lamba 1987, ya ruwaito Manzon Allah (saw) yana cewa: “Ku ji tsoron Allah a duk inda kuke.”
Wannan ke ƙara tabbatar mana da cewa, lallai babu abin da ya kai tsoron Allah fa’ida, domin kuwa a duk abin da mutum zai aikata wani al’amari, muddin ya ji tsoron Allah, to ba zai aikata assha ba. Kuma wannan ne zai sanya ya zama mutum nagari, mai amfanar kansa da sauran al’umma. Allah ya sa mu dace da daidai cikin tsoronsa, Amin.













