Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (10)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Shin Wane Ne Bahaushe Zalla A Yau?
Jama’a masu bibiyarmu a wannan muƙala, a wannan karon za mu duba wannan tambaya ta sama mai cewa, shin a wannan zamani da muke ciki ƙarni na 21, bisa la’akari da gamewa da dunƙulewar duniya zuwa wata ‘yar tsuƙaƙƙiyar da’ira, wane ne za a ƙalla, tashi ɗaya a kira shi da Bahaushe zalla?
Me ya kawo wannan tambaya? Babban dalilinta, shi ne yadda a yau muka wayi gari da ɓullowar wata bahaguwar ƙungiya, mai zimmar dawo da hannun agogo baya, wacce ta ɓoye da kishin Hausa amma a gefe ɗaya kuma take ƙunshe da wani mugun nufi mai haɗarin gaske ga zamantakewar al’umma.
A yau dai, duk inda ka duba al’ummar Arewacin Najeriya, aƙalla za a iya cewa cikin mutum goma, guda tara da Hausa suke magana (sosai) duk kuwa da cewa asalinsu ba Hausawa ba ne, suna da yarukansu na asali. Kada mu mance, a Arewacin Najeriya, akwai yaruka iri daban-daban fiye da 300.
Wani abin da zai ba ka mamaki ma shi ne, wasu yarukan ma, tuni Hausa ya haɗiye su. Wasu yaren, musamman ‘ya’yansu da jikoki, ba su iya ko gaisuwa ba da yarensu – sai dai Hausa. A Arewa, kusan kowa BAHAUSHE ne ta fuskar yare na zahiri. Idan da za ka samu Bafillace ko Babarbare ko Buzu da sauransu, waɗanda kakanninsu ba su iya Hausa ba, amma a yau da ka tambaye su batun yare, za su ce maka su HAUSAWA ne – saboda ba su da wani yare da suka iya idan ba Hausar ba.
Haka al’amarin yake a ƙasashe da dama, musamman a Afirka ta Yamma, ƙasashe kamar Nijar, Ghana, Kamaru, Chadi da makamantansu. Kusan duk wanda ka ji yana magana da Hausa, aƙalla yana da wani yare nasa na gado – amma bai iya ba, Hausa ta ƙwace shi.
To, a nan za mu dawo kan batun baya, shin me ya sa masu ƙumajin HAUSAWA ZALLA suke ƙulafuci da kafa ƙahon zuƙa ga Fulani kawai, har ma suna aibata Shehu Ɗanfodiyo? A nan za mu fahimta da cewa, da biyu, wai an bugi biri da rani. Kada mu manta, idan dai don kishin Hausa ne, to ai kamar yadda lamarin yake a zahiri – kusan kowa Bahaushe ne a yau, musamman a Arewa. Amma me ya sa ake taƙaita batun tsakanin HAUSAWA da FULANI? Amsa guda ɗaya ce – ana son hargitsa al’ummar Arewa. Ana son dasa gaba da ƙiyayya marar dalili tsakanin al’ummar Arewa.
Haka kuma idan dai domin samar da haɗin kai da taimakon al’umma ne ya sa suke wannan haƙilo, to ai a wannan zamanin ba da makamin ƘABILANCI za a bi ba, domin kuwa akwai wani babban jigo mai matuƙar tasiri, wanda tun farko shi ne ya haɗa kan al’umma kuma shi ne ma ya haɓaka da inganta ɗabi’un Hausawa da Fulani da ma duk wanda ya rungume shi, wato ADDININ MUSULUNCI.
Me ya sa na ce Addini ya fi Ƙabilanci tasiri? Tun farko kusan duk Bahaushen da ka samu a Arewacin Najeriya, Musulmi ne, ƙalilan ne suke cikin wani addini na daban. Haka kuma kusan duk Bafulatanin da ka gani, Musulmi ne, sai ƙalilan su ma da suke cikin wasu addinai na daban. Don haka Musulunci, bisa ga tsarinsa mai kyau, ya haramta ƘABILANCI amma ya ƙarfafa haɗin kai, zaman lafiya da zamantakekeniya a tsakanin al’umma. Don haka Hausawa da Fulani, sun zama ‘yan uwa na har abada ta fuskar MUSULUNCI. Sun yi auratayya, sun kafa iyali masu tsawon tarihi. Don haka, raba su a wannan zamani da sunan ƘABILANCI, abu me mai matuƙar wuya, tamkar dai ɗaukar Dala ba gammo. Haka kuma, al’amarin – ƘABILANCI – Abu ne mai matuƙar haɗari, wanda zai haifar wa al’umma alkaba’in da ba mu da mizanin auna muninsa. Allah ya kyauta – Amin.
Masu bibiyar wannan muƙala da haƙuri, a nan za mu tsaya, amma in sha Allahu a muƙala ta gaba, za mu bijiro da maudu’in: Ƙabilanci Sam, Zaman Lafiya Maraba. Mu huta lafiya.
_______________













