• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Monday, April 6, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (4)

TSOKACI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
January 2, 2026
in Gizago
0
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (4)

Bashir Yahuza Malumfashi, yayin da yake gabatar da ƙasida a Bikin Ranar Marubutan Hausa Ta Duniya, da ya gudana a Jigawa, shekaranjiya

32
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (4)

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

April 3, 2026
Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso

Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso

March 29, 2026
Bashir Yahuza Malumfashi, yayin da yake gabatar da ƙasida a Bikin Ranar Marubutan Hausa Ta Duniya, da ya gudana a Jigawa, shekaranjiya

 

                      __________
√ Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Batun Ramuwar Gayya:
Ya ku ‘yan uwa masu bibiyar wannan muƙala da jimiri, a wannan fitowa kashi na huɗu, za mu ci gaba da bayani dangane da wasu munanan manufofi da muka ankara da su daga ‘ya’yan Ƙungiyar Hausawa Bogi, musamman yadda suke nuna su a kafafen sadarwa na zamani (Soshalmidiya).

Ga duk mai tu’ammali da waɗannan kafafe, babu shakka zai riƙa gamuwa da munanan kalaman masu ƙumajin kafa Ƙungiyar Hausawa Zalla. Ɗaya daga cikinsu shi ne, za su kafa wannan ƙungiya ce, kacokan da nufin haddasa gaba da ƙiyayya tsakanin al’ummar Arewa, musamman ma dai tsakanin Fulani da Hausawa. Babbar manufarsu ita ce, ramuwar gayya da ɗaukar fansa a kan musamman Fulani.

A ƙoƙarinsu na bayyana wannan muguwar manufa, ƙarara za ka ji sun kama sunan Mujaddadi Usman Ɗanfodiyo, suna zagin shi da tozarta shi; sannan kuma suna ƙirƙirar tarihin ƙarya suna jingina masa. Ba shi kaɗai ba, masu wannan ƙungiya ta Hausawa zalla, za ka ga suna ta haƙilon haddasa gaba da husuma tsakanin al’ummar Musulmi. Su a nufinsu, al’ummar Fulani gaba ɗayansu ‘yan ta’adda ne, don haka ya kamata Hausawa su tashi su yaƙe su gaba ɗaya.

To, abin tambaya a nan shi ne, shin anya kuwa akwai alheri ga ƙungiyar da take bijiro da irin waɗannan baƙaƙen halaye? Shin da gaske ne, cewa Sheikh Usman Ɗanfodiyo (ra) bai shuka alheri ba a ƙasar Hausa? Shin wai ma da suke kiran dukkan Fulani da sunan ‘yan ta’adda, musamman kasancewar wasu daga cikinsu suna garkuwa da mutane da ta’addanci a yankin nan, shin a rigar ƙungiyoyin Fulani suke gudanar da wannan ta’addanci? Shin wannan ta’addanci da wasu baragurbin Fulani suke aikatawa, Hausawa kaɗai suke kamawa da kashewa?

Za mu bi tambayoyin nan ɗaya bayan ɗaya, inda da yardar Allah, za mu ida fahimtar gaskiyar manufar masu ƙungiyar Hausawa, cewa ba wani abu suke ɗauke da shi ba sai babbar guba da dasisar wargaza al’ummar da ke zaune lafiya da juna na tsawon zamani.

Game da Sheikh Usman Ɗanfodiyo (ra) kuwa, babu shakka, duk wani mai kyakkyawan tunani, musamman idan dai shi Musulmi ne na ƙwarai; to ba zai taɓa kushe Mujaddadi ba. Domin kuwa Sheikh ya kafa babban tarihi, abin yabawa a duniyar Musulunci. Daular Muslunci ta Sakkwato da ya kafa, tun kimanin sama da shekara 200 da ta gabata, ta kasance daula mafi girma da bunƙasa a Afrika ta Yamma.

Ya jaddada Musulunci. Ya yaɗa ilimi. Ya kafa gwamnati mai tsari, abin alfaharin baƙar fata, tun kafin zuwan Turawa. Ya kafa tsarin tafiyar da al’umma mai cike da adalci da ɗa’a da nagarta – wanda har zuwa yau ana cin gajiyarsa.

Jama’a, yau ma a nan zan dakata. Sai kuma karo na gaba, in sha Allahu. A ci gaba da bibiyar mu da haƙuri. Muna kuma maraba da dukkan martani, ƙarin bayani ko tambaya a Comment Section.
_______________

Previous Post

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawa Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (3)

Next Post

Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci

Related Posts

JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista
Gizago

JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

April 3, 2026
Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso
Gizago

Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso

March 29, 2026
Shin An Sallami Malam El-Rufa’i Ke Nan Ko Zai Dawo Shari’a?
Gizago

Shin An Sallami Malam El-Rufa’i Ke Nan Ko Zai Dawo Shari’a?

March 28, 2026
Next Post
Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci

Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Dokta Ɗanjuma Ya Tallafa Wa Mabuƙata Da Naira Miliyan 22

Dokta Ɗanjuma Ya Tallafa Wa Mabuƙata Da Naira Miliyan 22

June 30, 2023
TAURARON GIZAGAWA: NURA ADAMU AHMED

TAURARON GIZAGAWA: NURA ADAMU AHMED

August 3, 2023
A LOKACIN DA AL’UMMA KE CIKIN BAƘIN TALAUCI: Wani Gwamna Yana Gina Aljannar Duniya

A LOKACIN DA AL’UMMA KE CIKIN BAƘIN TALAUCI: Wani Gwamna Yana Gina Aljannar Duniya

January 30, 2024
SAKAMAKON FARKO NA GASAR RUBUTUN HAUSA TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

SAKAMAKON FARKO NA GASAR RUBUTUN HAUSA TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

December 1, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (9)
  • JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles

Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles

April 5, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (9)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (9)

April 4, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.