ƘUNGIYAR HAUSAWA ZALLA: TA INA ZA A FARA KUMA DA WACE MANUFA? (2)
Daga Yahuza Malumfashi

Haƙƙin Kafa Ƙungiya:
Ɗaya daga cikin tambayoyin da na bijiro da su a gabatarwa ita ce, shin ko al’ummar Hausawa zalla suna da ‘yancin kafa ƙungiya a Najeriya? To, in sha Allahu yanzu zan ɗan yi ƙoƙarin amsa ta, tare da ɗan tsokaci madaidaici.
Tabbas, ba wai Hausawa zalla ba, duk wani ɗan ƙasa yana da ‘yancin kafawa ko shiga cikin kowace ƙungiya da yake muradi, domin kuwa Sashi na 40 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima) ne ya ba shi wannan ‘yancin.
Ga abin da wannan Sashe na 40 yake cewa: “Kowane mutum yana da ‘yancin haɗa taro da sauran mutane kuma musamman zai iya kafawa ko kuma ya shiga cikin kowace jam’iyyar siyasa, ko ƙungiya, domin kare muradunsa. Sai dai kuma wannan ‘yanci ba zai ci karo da ikon da Kundin Tsarin Mulkin nan ya ba Hukumar Zaɓe ta Ƙasa Mai Cin Gashin Kanta ba, dangane da abin da ya shafi jam’iyyun siyasa, wanda hukumar ba ta amince da shi ba.”
Ke nan Tsarin Mulkin Najeriya ya amince wa ‘yan ƙasa kuma ya ba su ‘yancin yin taro cikin lumana, ko su kafa ƙungiya, misali ta ƙabila, ko addini, ko siyasa, ko ta sana’a, ko kuma ta kare muradun ma’aikata da makamantansu.
Bisa ga doron doka da ‘yancin ɗan ƙasa, al’ummar Hausawa zalla, kamar sauran ƙabilu, suna da ‘yancin kafa ƙungiyar kare muradunsu, kamar dai yadda sauran ƙabilu, misali Fulani, Yarabawa, Ibo da sauransu suke kafawa.
Sai dai kuma, kamar yadda masana al’amuran Shari’a da Tsarin Mulki suka sha nanatawa, inda haƙƙin wani ɗan ƙasa ya fara, nan kuma haƙƙin wani ɗan ƙasar yake tsayawa. Ma’ana dai, duk ƙungiyar da za a kafa, dole ne ta kasance bisa doron doka da odar ƙasa. Dole ta kasance mai manufar zaman lafiya da mutunta sauran al’ummar ƙasa.
Nan zan ɗiga aya a yau. Mu tarbi kashi na gaba, domin tattauna tambaye ta gaba mai cewa, shin da wace manufa ake son kafa Kungiyar Hausawa Zalla?
__________
Bashir Malumfashi, shi ne Editan Mujallar Taskar Gizago (online)












