KO ME YA SA MABIYA PETER OBI SUKA RIƘA MURNAR MUTUWAR HON. EKENE ABUBAKAR ADAMS?

Na karanta wani abin baƙin ciki da takaici a shafin Reno Omokri, inda na ga wasu mutane, waɗanda ‘yan ƙabilarn Igbo ne kuma magoya bayan ɗan takarar shugabancin ƙasa Peter Obi suna murna da munanan addu’o’i, saboda mutuwar Ɗan Majalisar Tarayya, mai ,wakiltar ƙananan hukumomin Chikun da Kajuru a Jihar Kaduna, Hon. Ekene Abubakar Adams.
Wani abin da ya ɗaure mani kai shi ne, mutumin nan fa ɗan Jam’iyyar Labour Party ne, jam’iyyar da suke goyon baya saboda ɗan uwansu Inyamuri (Peter Obi). To me ya sa suke murna da mutuwar sa?
Haka kuma, kamar yadda na samu labari, marigayi Adams, ɗan siyasa ne Mutumin-Mutane, wanda mutanen mazaɓarsa suke matuƙar ƙauna, saboda yana kyautata masu sosai. Hasali ma, dalilin kirkinsa ne ya sa suka zaɓe shi, a baƙuwar jam’iyya.
Tun da farko ma ya yi takarar Primary ne a Jam’iyyar APC amma aka kayar da shi. Dalili ke nan ya koma Jam’iyyar Labour Party kuma jama’a suka bi shi can suka zaɓe shi. Yana cikin wakilci mai nagarta, Allah Ya jarabce shi da rashin lafiya, ya mutu.
A ɗan nazarin da na yi, babban abin da ya sa Inyamurai suka yi murna da mutuwar sa, sun yi zaton shi MUSULMI ne, saboda sunan ABUBAKAR da suka gani a jikin jerin sunansa. Haka kuma sun yi murna ne saboda shi ɗan Arewa ne kuma sun yi zaton shi ɗan Jam’iyyar APC ko PDP ne, alhali ɗan jam’iyyarsu ne kuma ba Musulmi ba ne, shi Kirista ne.
Wannan abin takaici ne matuƙa. Saboda me mutane za su yi murnar mutuwar wani mutum saboda bambancin addini da yanki?
To yanzu da a ce Peter Obi ne ya zama Shugaban Kasa, yaya al’ummar Igbo za su riƙa yi wa sauran ‘yan Najeriya?
Allah Ya kyauta.













