ZUMUNCI: Ƙungiyar Ɗalibai Ta Karrama ACC Tasi’u Saulawa


Membobin Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makarantar Firamaren Gwaji ta Nagogo (Zangon Karatu na Shekarar 1991) da ke birnin Katsina sun gudanar da ƙwarya-kwaryan taro, inda suka karrama ɗaya daga cikinsu, Tasi’u Sanusi Saulawa.
Ƙungiyar ta karrama Tasi’u ne domin taya shi murna, bisa samun ƙarin girma zuwa Mataimakin Babban Kwantirola (ACC) a Hukumar Kwastam.
Da yake jawabi a yayin karramawar, Shugaban ƙungiyar, Malam Aliyu Adamu ya bayyana cewa: “Alal haƙiƙa muna maka fatan alheri da addu’ar likkafa za ta ƙara gaba da yardar Allah.
“Don haka mu membobin wannan ƙungiya ta Ɗaliban Makarantar Nagogo, Zangon Karatu Na Shekarar 199 (NOBA) mun tabbatar da ka cancanci wannan sabon muƙami da aka ba ka, ba don komai ba sai saboda sadaukarwa da ka yi da yin aiki tuƙuru da kuma sanin ya kamata wajen gudanar da aiki.”
Shugaban ya ci gaba da cewa, “har wa yau dai muna ƙara taya ka murna. Ubangiji Allah Ya taya ka riƙo, Ya kuma shige maka gaba a duk inda ka samu kanka.”













