KISAN MAWAƘI MOHBAD: Darasi Da Jan Hankali G Al’ummar Arewa
Daga Yusuf Dingyaɗi

~~~~~~~
Yanzu ‘yan Arewa suna kallon yadda wani ɓangaren al’umma na Najeriya suka haɗu a cikin abin da bai fi kwanaki uku suna zanga-zanga tare da haɗin kai don neman tilasta wa mahukunta da sai sun yi bincike da hukunta masu hannu a kan kisan ɗan rawa kuma mawaƙi, Ilerioluwa Aloba, wanda aka fi sani da Mobad, wnda ake zargin ya rasa ransa a kwanan nan ta hanyar kisan gilla.
Mutum ɗaya ne waɗannan ɗaruruwan mutane daga Legas, Oyo, Ekiti, Osun da Ingila suka haɗu suna neman haƙƙinsa, a ƙasar da a kullum ake bayyana akwai alƙalluman da suke bayanin sai an kashe fiye da rayuka 40 zuwa 50 ko harin ta’addanci ko na kisan gilla ko ganganci na hatsarin mota ko shan ƙwayoyi da sauransu.
AREWA, mussaman Arewa Maso Yamma, a jihohin Sakkwato, Kebbi, Zamfara, Katsina da Neja da Kaduna, kusan kullum an yi zargin sai an yi kisan gilla na ganganci ko a wajen ‘yan ta’adda ko masu amfani da hanyoyin ramuwar gayya da sauran irinsu, fiye da ko’ina a cikin ƙasar nan.
Zubar da jini da kisan jama’a da sace dukiyoyinsu a yankin Arewa ta Yamma ya zama abin da ke faruwa a kullum.
Shin har yaushe za mu iya fitowa fili mu jagoranci juna don aika irin wannan saƙon ga mahukunta dangane da matsalar tsaro da kisan gillar da ake yi wa al’ummarmu a birane da karkara?
Yankunan karkara a jihohin Sakkwato, Zamfara, Katsina, Kaduna, Neja da Kebbi kusan kullum sai an kashe ko yin garkuwa ko satar dabbobi ko kisan gilla a cikinsu.
Har yaushe zamu aje siyasa, son kai da ƙin juna mu haɗu a Arewa a tare, mu yi wa kanmu da jama’armu mafita dangane da bayyana koke-kokenmu a fili, gaban duniya don fatan samun nasara, har mahukunta nan su juyo don bai wa lamarin matakin da ya dace?
Ba wani babba a Abuja ko a fadar gwamnati da zai iya ɗaukar wani matakin da zai kai na muryar jama’a mai ƙarfi.
A tashi tsaye a tare da yi wa juna uzuri da mayar da hankali ga yaƙar wannan lamarin, ba tare da tsoro ko shakka ko kwaɗayi a kan makomar da za ta zama a kan wannan lamarin ba.
Dole mu yi kishin ƙasa da son juna da yi wa juna uzuri tare da haɗin kai da adalci kan samar da makoma ne kawai mafita a nan gaba.
Addu’oi da neman da muke Allah Ya kawo mana sauƙi, zai zo muddin muka gyara da juna, muka aje siyasa da hassada da cin amana da rashin gaskiya don fuskantar wannan matsalar a cikin haɗin kai.
‘Yan AREWA, mu koyi darasi da haɗin kai don kuwa tafiya ta fara nisa; kusan duk waɗanda suka dace su yi mana magani, tasu fitinar ta ishe su!
ALLAH ga Arewa da ‘yan Arewa. Muna fatan mafita!
~~~~~~~
Yusuf Dingyaɗi, ɗan jarida, marubuci,ɗan siyasa, ya rubuto taokacin nan Sakkwato!
~~~~~~~













