Shin An Sallami Malam El-Rufa’i Ke Nan Ko Zai Dawo Shari’a?
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
A sakamakon rasuwar mahaifiyarsa, Hukumomin Tsaro sun saki Malam Nasir El-Rufaii, wanda haka zai ba shi damar zaman makoki.
Kafin a sake shi a jiya Juma’a, Malam Nasir yana tsare a hannun hukumar ICPC, inda yake fuskantar tuhumomi daban-daban da suka danganci kuɗi, a lokacin da yake Gwamnan Jihar Kaduna daga 2015-2023.
Kafin a samu wannan matsala, muhimman mutane uku a wannan gwamnati, suna jituwa da ɗasawa. Waɗannan kuwa sun haɗa da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, wanda El-Rufa’i ya yi iyaka ƙoƙarinsa, har sai da ya ga ya samu nasarar hawa wannan kujera ta Shugaban Ƙasa.
Akwai Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara ta Fuskar Tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu, wanda shi da Elrufa’i aminan juna ne a can baya. Sun yi aiki tare a Gwamnatin Obasanjo cikin aminci da juna.
Mutum na uku, shi ne Gwamnan Jihar Kaduna na yanzu, Sanata Uba Sani. Malam Nasir shi ne ya yi uwa kuma ya yi makarɓiya, ya tsaya masa ya zama Sanata a Jihar Kaduna, sannan kuma ya yi duk mai yiwuwa, ya ɗora shi kujerar mulki, ya gaje shi a matsayin gwamna.
Abin tambaya a nan shi ne, shin ko mutanen nan uku sun huce da fushin da suke da El-Rufa’i? Yanzu da suka sanya aka sake shi, shi ke nan ya shaƙi iskar ‘yanci, ko kuwa za a dawo a ci gaba da shari’a, idan an kammala zaman makoki?
Zuwa gare ku al’umma: Shin yaya kuke ganin wannan al’amari? Shin ya kamata a samu sasanci tsakanin El-Rufa’i da Gwamnatin Tinubu ko kuwa?
__________













