RAMADAN KARIM: 28-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Yau Talata, Allah ya nuna mana rana ta 28 a Ramadan. Yau ma ga nasiharmu:
‘Yan uwa, yau dai nasiharmu ta karkata ne ga nuni da muhimmancin taimakon mabuƙata. Yana da kyau kuma abu ne mai tasiri, mu riƙa taimakon mabuƙata.
Allah ya yi bayani a Suratu Ma’un 107:1-7, dangane da taimakon mabuƙata. Manzon Allah (saw), a Hadisin Imam Tabarani ya ce: “Mafi alheri… wanda ya fi amfani ga mutane.”
Ya Allah, ka sanya mu cikin masu zuciyar taimakon kuma ka yassare mana arzikin taimakon, Amin.
__________













