RAMADAN KARIM: 15-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Bayan haka, a yau Laraba, Allah ya nuna mana rana ta 15 a Ramadan. Yau ma ga ‘yar nasiha:
A yau za mu yi nasiha ne da jan hankali, dangane da munin da ke tattare da yaɗa jita-jita da zunɗe. Haka kuma da nuna muhimmancin rufa wa juna asiri.
Allah (swt) a cikin Suratun Nur 24:19, ya ce: “Lalle ne waɗanda suke son a yaɗa alfasha (munanan ayyuka ko zarge-zarge na fasiƙanci) a cikin muminai, suna da azaba mai raɗaɗi a duniya da kuma lahira. Kuma Allah ne ya sani, ku kuwa ba ku sani ba.”
Wannan aya ta sauka ne a lokacin labarin ƙage da aka yi wa Sayyida A’isha (RA). Tana nuna cewa son yaɗa jita-jita ko zargin alfasha a cikin al’umma babban laifi ne kuma yana jawo fushin Allah da azaba. Don haka mu guji yaɗa jita-jita ko yin zunɗe ga junanmu.
Hadisin Sahih Muslim mai lamba 2699, daga Abu Huraira (RA) ya ce, Manzon Allah (SAW) ya ce: “Duk wanda ya yaye wa wani mumini wata damuwa daga cikin damuwoyin duniya, Allah zai yaye masa wata damuwa daga cikin damuwoyin ranar alƙiyama.”
Lallai ne mu kiyayi taɓa mutumcin juna, mu zamo masu yaye wa juna damuwa da rufa wa juna asiri, ba masu ƙara wa mutane lalura ba. Allah ya sa mu dace, Amin.
__________













