• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, April 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

Yunƙurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (14)

TSOKACI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
March 1, 2026
in Gizago
0
Yunƙurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (14)

Ta'addanci ba gadon wata ƙabila ɗaya ba ne

26
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Yunƙurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (14)

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

April 16, 2026
JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

April 3, 2026
Ta’addanci ba gadon wata ƙabila ɗaya ba ne

 

__________

√ Wani Salon Makirci Daga Hausawan Bogi

Yana daga cikin makirci da munafunci da alayen haddasa fitina na masu iƙirarin Hausa Zalla, yadda za ka ji suna yin kuɗin goro ga al’ummar Fulani, suna kiran su da ‘yan ta’adda.

A kullum za ka ji suna kiran shugabannin ƙungiyoyin Fulani da cewa wai su sanya baki, domin Fulanin Daji su daina ta’addanci amma kuma ba su yin kira ga gwamnati da ta ɗauki matakin da ya dace a kan DUK ‘YAN TA’ADDA da suka addabi al’umma a kowane sashi na ƙasar nan.

Abin tambaya shi ne, shin sun manta da cewa shi ɗan ta’adda babu ruwansa da ƙabila, addini ko sashin da mutum ya fito? Shin sun manta da cewa Shugabannin Fulani su ma gama-garin mutane ne da ba su da makami ko ikon hukunci a hannunsu?

Idan dai gaskiya ake so, to GWAMNATI ita ce mai iko. Ita take da makaman yaƙi, ita take da sojoji da ‘yan sanda da DSS da sauran jami’an tsaro.

Me zai hana gaba ɗaya mu nemi ita gwamnatin ta yi abin da ya dace?

Me zai hana gwamnatin ta yi bincike ta zaƙulo duk wani ɗan ta’adda da ke ƙasar nan, da mai ɗaure masa gindi, da mai samar masa da makami (kowane ne) ta kama shi, ta hukunta shi?

Mu dai har kullum ba za mu gushe ba, za mu ci gaba da faɗin gaskiya, cewa ta’addanci a ƙasar nan ba kayan wata ƙabila ɗaya ba ne. Aiki ne na bijirarrun mutanen da suka sanya kansu cutar da al’umma. A kowace ƙabila, akwai ‘yan ta’adda.

Don haka a daina yin kuɗin goro. WANDA DUK YA YI LAIFI, ko shi ɗan wace ƙabila ne, ko shi wane addini yake bi, ko daga wace shiyya yake, AIKIN GWAMNATI ne ta kama shi ta hukunta shi, daidai da laifinsa. Wannan shi ne adalci kuma shi zai kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali a ƙasa.

Lallai ne mu sani, rashin hukunta masu laifi, shi ya sanya ta’addanci ya ta’azzara! Amma muddin gwamnati ta yi abin da ya dace, to babu shakka za a samu lafiya!

___________

Previous Post

RAMADAN KARIM: 12-1447

Next Post

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (2)

Related Posts

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa
Gizago

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

April 16, 2026
JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista
Gizago

JOS! JOS!! JOS: Muhimmin Saƙo Zuwa Ga Musulmi Da Kirista

April 3, 2026
Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso
Gizago

Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso

March 29, 2026
Next Post
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (2)

FITILAR MATASA - Zannan Galadima (2)

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

JIDALIN KISHIYA – Labarin Uwargida Farida

JIDALIN KISHIYA – Labarin Uwargida Farida

September 3, 2024
INSECURITY IN NORTHERN NIGERIA: AN OPEN LETTER TO NSA NUHU RIBADU

TAƁARƁAREWAR TSARO A AREWA: BUƊAƊƊIYAR WASIƘA ZUWA GA MALAM NUHU RIBADU

August 8, 2025
Kishin Ƙasa Ne Tubalin Farko Na Gina Rayuwar Al’umma (2)

Kishin Ƙasa Ne Tubalin Farko Na Gina Rayuwar Al’umma (2)

June 29, 2023
Malumfashi Mun Yi Babban Rashi

Malumfashi Mun Yi Babban Rashi

March 26, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa
  • Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye
  • Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

April 16, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.