JIHAR KATSINA/MALUMFASHI MUN YI BABBAN RASHI

__________
Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un!
Labari ya ishe ni da safiyar nan, cewa Allah ya yi wa Alhaji Bello Musa Dankano rasuwa.
Malam Bello, shi ne Talban Galadiman Katsina, yaya ga Wazirin Galadiman Katsina, Alhaji Shehu Musa Ɗankano. Ya taɓa zama Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, a ƙarƙashin mulkin soja, Kamar Sama’ila Bature Chamah.
Malam Bello ƙwararren marubucin labarun ƙirƙira ne kuma marubucin waƙoƙin fasaha na Ingilishi.
Idan Allah ya kai mu anjima da ƙarfe 11 na safe, za a yi jana’izarsa a gidansa da ke Ƙofar Ƙaura, Katsina.
Muna roƙon Allah ya ji ƙan shi da rahama, ya sa ya huta. Mu kuma da muka rage, Allah ya kyautata tamu, idan lokacin ya zo. Amin-Summa-Amin!
__________













