• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, January 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

Abin Da Ya Sa Na Naɗa Mataimaka 85 – Ciyaman Mukhtari City

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
September 18, 2025
in Labarai
0
Abin Da Ya Sa Na Naɗa Mataimaka 85 – Ciyaman Mukhtari City

A dama, Shugaban Ƙaramar Hukumar Malumfashi ne, Alhaji Mukhtar Abdullahi, tare da ɗaya daga cikin SA da ya naɗa a gwamnatinsa

26
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Abin Da Ya Sa Na Naɗa Mataimaka 85 – Ciyaman Mukhtari City

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Bura women Celebrate Bukar Usman at 83

Ƙungiyar Matan Al’ummar Bura Sun Karrama Dr. Bukar Usman Bisa Cika Shekaru 83

January 9, 2026
Sojoji Sun Ƙwato Muggan Makamai A Jihar Taraba

Sojoji Sun Ƙwato Muggan Makamai A Jihar Taraba

January 5, 2026
Wasu daga cikin Mataimakan da aka nada a Ƙaramar Hukumar Malumfashi

 

                           __________

Shugaban Ƙaramar Hukumar Malumfashi a Jihar Katsina, Alhaji Mukhtari Abdullahi City ya bayyana cewa ya naɗa mataimaka manya da ƙanana su 85 a gwamnatinsa ne domin kusanto da al’umma ga gwamnati.

Shugaban ya faɗi haka ne a wata gajeruwar tattaunawa da wakilinmu ta wayar tarho. Ya bayyana cewa ya naɗa mutane 30 a matsayin Manyan Mataimaka (SSA) bisa umurnin Gwamna Malam Dikko Umar Yadda, a yayin da ya naɗa mutane 55 don ƙashin kansa, a matsayin Ƙananan Mataimaka (SA).
“Ita harkar gwamnati ta jama’a ce, don haka na zaɓo mutanen da suke tare da jama’a kuma suke taya mu hidima a siyasa, domin su taimaka wajen tafiyar da sha’anin nan na mulkin al’umma.” Inji Ciyaman Mukhtar.

Ya ƙara da cewa, zai yi aiki da su ne a matsayin mashawarta, yadda su za su kasance idon al’umma a gwamnatinsa. Ya ce, “na umurce su da su yi aiki kafaɗa-da-kafaɗa da dukkan kansilolinmu, yadda za su riƙa binciko mana irin aikin da ake buƙata a kowace mazaɓa. Ta hakan za mu samu sauƙin tafiyar da aiki, tare da bunƙasa al’umma na kowane lungu a ƙaramar hukumar Malumfashi.”

Shin an ɗauke su a matsayin cikakkun ma’aikata da cikakken albashi, kuma nawa ne za a riƙa biyansu? Tambayar da wakilinmu ya yi wa Ciyaman ke nan, inda shi kuma ya amsa da cewa, “Ba cikakkun ma’aikata ba ne. Suna kan tsari ne na mataimaka, kamar yadda al’amarin yake a kowace gwamnatin siyasa. Kuma ba albashi za a riƙa ba su ba. Manyan Mataimakan, za a riƙa ba su alawus na Naira dubu hamsin, yayin da su kuma Ƙananan Mataimaka za a riƙa ba su Naira dubu talatin duk wata.”

Sai dai jim kaɗan da kammala taron naɗin, ɗaya daga cikin waɗanda aka naɗa, Malam Isma’ila A. Sanda ya sanar da ajiye mukamin nasa. Da yake bayyana wannan mataki a shafinsa na Facebook, ya bayyana cewa:

A hagu, Shugaban Ƙaramar Hukumar Malumfashi ne, Alhaji Mukhtar Abdullahi, tare da Malam Isma’il A. Sanda

“Da farko dai ina miƙa saƙon godiya ga mai girma Shugaban Ƙaramar Hukumar Malumfashi, Hon. Mukhtar Abdullahi City, a kan muƙami da ya ba ni na Mai Taimaka Masa Na Musamman (S.A).

“Na biyu, ina mai sanar da Shugaban Ƙaramar Hukuma na aje wannan muƙami da ka ba ni, bisa ƙashin kaina ba tare da na yi shawara da kowa ba. Amma na so a ce an sanar da ni kafin a ba ni muƙamin, da sai in ba da sunan wani a cikin mutanena; kawai sai na ji kwatsam an aiko mani da takardar. Duk da haka ina godiya da har ka tuna da ni a cikin matasan da suka ba ka gudunmuwa a lokacin yaƙin neman zaɓenka a matsayin Shugaban Ƙaramar Hukuma.”
_______________

Previous Post

Hukumar NDLEA Ta Kama Ɗan Indiya Da Muggan Ƙwayoyi Na Naira Biliyan 3.9

Next Post

Yan Bindiga Sun Sako Miji Da Matarsa Bayan An Biya Naira Miliyan 50

Related Posts

Bura women Celebrate Bukar Usman at 83
Labarai

Ƙungiyar Matan Al’ummar Bura Sun Karrama Dr. Bukar Usman Bisa Cika Shekaru 83

January 9, 2026
Sojoji Sun Ƙwato Muggan Makamai A Jihar Taraba
Labarai

Sojoji Sun Ƙwato Muggan Makamai A Jihar Taraba

January 5, 2026
Hukuncin Nnamdi Kanu: Minista Bianca ta Nemi Igbo Su Guji Tada Fitina
Labarai

Hukuncin Nnamdi Kanu: Minista Bianca ta Nemi Igbo Su Guji Tada Fitina

November 22, 2025
Next Post
Yan Bindiga Sun Sako Miji Da Matarsa Bayan An Biya Naira Miliyan 50

Yan Bindiga Sun Sako Miji Da Matarsa Bayan An Biya Naira Miliyan 50

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

UAE Lifts Ban On Nigerian Travellers

UAE Lifts Ban On Nigerian Travellers

September 12, 2023
TAKAICI: Waɗannan… Duk A Cikin Mako Ɗaya?

TAKAICI: Waɗannan… Duk A Cikin Mako Ɗaya?

November 20, 2025
The World Converge and Pay Final Respects to Late President Muhammadu Buhari at Daura Burial

The World Converge and Pay Final Respects to Late President Muhammadu Buhari at Daura Burial

July 16, 2025

Ɗan Kasuwa Ya Koka Da Rusau A Kano

June 25, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation
  • Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
  • Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.