Abin Da Ya Sa Na Naɗa Mataimaka 85 – Ciyaman Mukhtari City
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Shugaban Ƙaramar Hukumar Malumfashi a Jihar Katsina, Alhaji Mukhtari Abdullahi City ya bayyana cewa ya naɗa mataimaka manya da ƙanana su 85 a gwamnatinsa ne domin kusanto da al’umma ga gwamnati.
Shugaban ya faɗi haka ne a wata gajeruwar tattaunawa da wakilinmu ta wayar tarho. Ya bayyana cewa ya naɗa mutane 30 a matsayin Manyan Mataimaka (SSA) bisa umurnin Gwamna Malam Dikko Umar Yadda, a yayin da ya naɗa mutane 55 don ƙashin kansa, a matsayin Ƙananan Mataimaka (SA).
“Ita harkar gwamnati ta jama’a ce, don haka na zaɓo mutanen da suke tare da jama’a kuma suke taya mu hidima a siyasa, domin su taimaka wajen tafiyar da sha’anin nan na mulkin al’umma.” Inji Ciyaman Mukhtar.
Ya ƙara da cewa, zai yi aiki da su ne a matsayin mashawarta, yadda su za su kasance idon al’umma a gwamnatinsa. Ya ce, “na umurce su da su yi aiki kafaɗa-da-kafaɗa da dukkan kansilolinmu, yadda za su riƙa binciko mana irin aikin da ake buƙata a kowace mazaɓa. Ta hakan za mu samu sauƙin tafiyar da aiki, tare da bunƙasa al’umma na kowane lungu a ƙaramar hukumar Malumfashi.”
Shin an ɗauke su a matsayin cikakkun ma’aikata da cikakken albashi, kuma nawa ne za a riƙa biyansu? Tambayar da wakilinmu ya yi wa Ciyaman ke nan, inda shi kuma ya amsa da cewa, “Ba cikakkun ma’aikata ba ne. Suna kan tsari ne na mataimaka, kamar yadda al’amarin yake a kowace gwamnatin siyasa. Kuma ba albashi za a riƙa ba su ba. Manyan Mataimakan, za a riƙa ba su alawus na Naira dubu hamsin, yayin da su kuma Ƙananan Mataimaka za a riƙa ba su Naira dubu talatin duk wata.”
Sai dai jim kaɗan da kammala taron naɗin, ɗaya daga cikin waɗanda aka naɗa, Malam Isma’ila A. Sanda ya sanar da ajiye mukamin nasa. Da yake bayyana wannan mataki a shafinsa na Facebook, ya bayyana cewa:

“Da farko dai ina miƙa saƙon godiya ga mai girma Shugaban Ƙaramar Hukumar Malumfashi, Hon. Mukhtar Abdullahi City, a kan muƙami da ya ba ni na Mai Taimaka Masa Na Musamman (S.A).
“Na biyu, ina mai sanar da Shugaban Ƙaramar Hukuma na aje wannan muƙami da ka ba ni, bisa ƙashin kaina ba tare da na yi shawara da kowa ba. Amma na so a ce an sanar da ni kafin a ba ni muƙamin, da sai in ba da sunan wani a cikin mutanena; kawai sai na ji kwatsam an aiko mani da takardar. Duk da haka ina godiya da har ka tuna da ni a cikin matasan da suka ba ka gudunmuwa a lokacin yaƙin neman zaɓenka a matsayin Shugaban Ƙaramar Hukuma.”
_______________












