Tarihin Ƙungiyar Hamas
Daga Umar Labdo Muhammad
~~~~~~~
Ƙungiyar Hamas ta samo asali daga Ƙungiyar Ikhwanul Muslimun ta ƙasar Masar.
A shekara ta 1935, Ƙungiyar Ikhwan ƙarƙashin jagorancin Hassan Albanna ta fara gudanar da tuntuɓa a yankin Falasɗinu da nufin kafa reshenta a yankin.
Bayan tattaunawa da matasa da ɗalibai, wanda ya ɗauki shekaru, an kafa reshen ƙungiyar na farko a shekarar 1945 a birnin Ƙudus. Kuma a ranar 25 ga watan Nuwamba, 1956 an buɗe babban ofishin ƙungiyar a birnin Gazza.
Bayan sama da shekaru 60 tana gudanar da ayyukanta, a matsayin reshe na yKungiyar Ikhwan da cibiyarta take a ƙasar Masar, Ƙungiyar Hamas ta yi shelar tsinke alaƙarta da Ikhwan a shekara ta 2017, don ta samu damar ci gaba da aikinta na jihadi da cikakken ‘yanci.
Ana ɗaukar Sheikh Ahmad Yasin a matsayin wanda ya assasa Ƙungiyar Hamas. Daga cikin sanannun shugabanninta akwai Khalid Mish’al, wanda ya daɗe yana jagorantar ɓangaren ƙungiyar na siyasa da Yahya Sinwar da Abdul Aziz Rantisi da Isma’il Haniyya.
Ƙungiyar Hamas tana da ɓangarori biyu: ɓangaren siyasa, wanda yake shiga zaɓe a Majalisar ƙasa ta Falasɗinu da ɓangaren soji, da suke kira da sunan Bataliyar Izzuddeen Alƙassam, wanda sunan wani dakare ne da ya fara ƙaddamar da gwagwarmaya da makami a kan Daular Bani Yahudu, tun farkon kafa ta. Wannan sashe na Hamas, shi ke ƙaddamar da aikin jihadi a kan ƙasar Isra’ila, ciki har da yaƙin da ake ciki yanzu, wanda aka yi wa laƙabi da Ambaliyar Aƙsa.
Ɓangaren Hamas na siyasa yana tafiyar da al’amuransa a bayyane, saɓanin Bataliyar Izzuddeen Alƙassam, wacce take tafiyar da ayyukanta a sirri.
A yau shi ke mulkin Zirin Gaza kuma yana cikin siyasar Daular Falasdyinu mai ƙwaryaƙwaryan cin gashin kai. Yana cikin wannan siyasa tsundum kuma a Majalisar Ƙasar Falasɗinu, shi ya fi kowace ƙungiya da jam’iyya yawan wakilai, ciki har da Ƙungiyar Fatah ta Shugaba Mahmoud Abbas.
Babu taƙamaimai dangane da adadin mayaƙan Hamas amma majiyoyi da yawa suna nuni da cewa ƙungiyar tana da zaratan mayaƙa kimanin 15,000, ban da wasu daban da ake iya kira su ɗauki makami idan buƙata ta gilma.
Hamas ta mallaki makamai nau’i dabam-daban, musamman rokoki masu cin zango mai nisa da matsakaici da manyan bindigogi da ƙananan jirage da ake sarrafawa daga nesa da kuma abin da ta ba Isra’ila mamaki da shi a wannan yaƙin, watau baburan sama masu ɗaukar mayaƙa kuma su yi wa na’ura mai hangen jiragen sama (radar) layar zana.
Babbar manufar Ƙungiyar Hamas ita ce ‘yanta kafatanin ƙasar Falasɗinu da fito-na-fito da manufar Sahyuniyya ta ƙwace ƙasa da kore Falasɗinawa daga ƙasarsu ta gado.
Kamar yadda mai karatu zai yi zato, wasu manyan ƙasashen duniya suna ɗaukar Hamas a matsayin ƙungiyar ta’addanci. Waɗannan ƙasashe sun haɗa da babbar algunguma, ƙasar Amurka da Burtaniya da Tarayyar Kasashen Turar da Japan da Usturaliya, da sauransu.
~~~~~~~













