Amina Gambo Ta Yi Bankwana Da Freedom Radio
Ma’aikaciyar Gidan Rediyon Freedom, Kano, Amina Gambo Adam ta bayyana cewa ta kammala aiki da gidan rediyon, bayan tsawon shekara shida a matsayin jami’a mai gabatar da shirye-shirye.
Kamar yadda ta wallafa a shafinta na Facebook, ta ce: “Bayan tsawon shekara bakwai da zuwa Tashar Freedom a matsayin Ɗalibar Koyon Makamar da kuma tsawon shekara shida a matsayin Ma’aikaciya mai gabatar da shirye-shirye a tashar Freedom Radio, na ajiye aikina a kafar, domin ci gaba da buɗe wani sabon shafi a rayuwata a ɓangaren aiki.”
Ta ƙara da cewa: “Na gode wa Allah ( S.W.A) da iko da damar da ya ba ni ta yin wannan aiki a lokacin da ya so, ya kuma nufe ni da ajiyewa a lokacin da ya so. Ina godiya ga wannan kamfani da abokan aikina bisa ilimin aiki da na darasin zaman rayuwa da na samu a tsawon zamana da su.
“Ina mai farin cikin miƙa godiya gare ku masoyana, ‘yan uwa da abokan arziki. In sh Allah ba mu rabu ba, za mu ci gaba da kasancewa tare a rayuwa ta gaba.”
Malama Amina ta kammala jawabinta da addu’a, tana cewa: “Allah Ya taimake mu a kan dukkanin abin da muka saka a gaba, ya kare mu daga dukkan abin ƙi. Amin, na gode!”














Tabbas bankwana wani abune meratsa zuciyar masoya nima nayi kewarki