Daga Bashir Yahuza Malumfashi
A yau Juma’a, 27-11-1444 (Hijriyya), 16-06-2023 (Miladiyya), a yayin Sallar Jumu’a a Masallacin Eriya Malumfashi, wacce Liman Malam Mustapha Tahir ya jagoranta, ya gabatar da huɗuba game da muhimmancin Sunna da illar Bidi’a.
Liman ya fara da bayyana ma’anar Sunna a Addinin Musulunci, cewa ita ce duk wani aiki da Manzon Allah (saw) ya aikata ko ya yi umurni da a aikata ko kuma ya gani ana aikatawa amma bai hana ba.
Sannan kuma ya bayyana ma’anar Bidi’a da cewa ita ce wani aiki da Manzon Allah bai yi ba, bai ba da umarni a aikata ba, kuma bai gani ana aikatawa amma ya ƙyale ba.
Malam ya kwaɗaitar da al’umma da su riƙe Sunna ƙamkam, domin kuwa Addinin Allah ya cika, Manzon Allah (saw) ya isar da saƙo dukkansa, bai rage komai ba. Musulunci ya tanadar da tsarin yadda mutum zai yi bauta da yadda zai yi rayuwa. Yadda mutum zai Salla, Azumi, Zakka, Hajji da kuma yadda zai inganta riƙo da Tauhidi, duk an tanadar. Haka kuma daidai da yadda mutum zai yi kashi da fitsari ko yadda zai saka sutura, da yadda zai yi rayuwa dukkanta, Annabi Sallallahu alaihi Wasallama ya koyar. Saura mutum ya tashi ya nemi ilimi kawai.
Malam ya ce duk wanda ya yi riƙo da wata Sunna kuma wani ya yi koyi da shi, to zai tabbata cikin ladar har zuwa tashin ƙiyama. Haka kuma duk wanda ya riƙi Bidi’a har wani ya yi koyi da shi, to zai tabbata cikin girbar zunubi har zuwa ranar tashin ƙiyama, kuma a haɗa masa da kamashon zunubin wanda ya yi koyin da shi.
Malam ya kafa hujja da Hadisin Nana A’isha (ra), cewa duk wanda ya haddasa wani aiki da ba umurnin Allah da ManzonSa ba, to an mayar masa. Don haka ya jaddada cewa, lallai Sunna dukkanta alheri ce, sai mu aikata ta. Sannan dukkan Bidi’a dukkanta sharri ce, sai mu guje mata.
Haka kuma Malam ya ja hankalin al’umma da cewa, Manzon Allah (saw) ya ce a lokacin da al’umma suka lalace, to duk wanda ya riƙi Sunna, yana da wata lada ta musamman.
Ya sanar da mu cewa babu shakka Ajanna gaskiya ce. Allah Ya tanade ta ga bayinSa na ƙwarai masu aikata aikin alheri kuma Ya kwaɗaitar da a neme ta ta aikin ƙwarai. Haka kuma Wuta gaskiya ce, Allah Ya tanade ta domin kangararru, don haka mu guje ta. “Wanda duk ya aikata kyakkyawan aiki daidai da ƙwayar zarra, zai gani. Haka kuma wanda duk ya aikata mummuna, daidai da ƙwayar zarra, zai gani.”
Allah Ka yi mana jagora a rayuwa, Ka tabbatar da mu cikin Musulunci, Ka sa mu cika da imani, idan lokacin mutuwarmu ya zo. Amin!














Allah ya sakada alkhairi dan malumfashi BASHIR YAHUZA
Amin Amin Ya Allah. Ni ma na gode kwarai.
Masha Allah. Allah Ya sa ka da alheri. Mu na godiya da wannan tunatarwa.
Ma sha Allah.
Madalla. Mu ma mun gode.
Amin Malam.