Janar Buratai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne
– Oba Adekunle Makama
Daga Bashir Yahuza Malumfashi
__________
Mai martaba, Olowu na Al’ummar Owu-Kuta, Dakta Adekunle Makama Oyelude, CON kuma Tegbosun III, ya bayyana cewa tsohon Shugaban Rundunar Sojojin Ƙasa ta Najeriya, Laftanar-Janar Tukur Yusuf Buratai, CFR (mai ritaya), tsohon Jakadan Najeriya a Jamhuriyar Benin, Betaran Biu kuma Garkuwan Keffi, mutum ne da za a iya kira da babban ɗan kishin ƙasa, musamman irin yadda yake mu’amalar alheri da dukkan alummomin da suke a faɗin Najeriya, har ma da na ƙasashen waje.
Mai sarauta Adekunle, wanda shi ne Mataimakin Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya na Jihar Osun, ya bayyana haka ne a wata tattaunawa da wakilanmu a garin Keffi, a yayin shagulgulan bikin auren A’isha Tukur Buratai da angonta, Umar Abba Zoru.
Da yake bayyana dangantakarsa da Janar Buratai, Oba Adekunle ya bayyana cewa: “Buratai aminina ne, amana ce ke tsakaninmu. Duk hidimarsa, ina ciki. Haka shi ma, duk hidimata yana ciki. Shi nagartaccen mutum ne, wanda ake dawwamammen zumunci da shi, ba tare da tsoron komai ba. Wannan shi ne babban dalilin amana da zumunci a tsakaninmu.”

Da ya juya kan ma’auratan, Oba ya ce: “Ita ɗiyarmu A’isha, ta samu tarbiyya mai kyau. Ina da yaƙinin ba za ta ba mijinta damuwa ba. Haka shi ma ango, ya fito daga gidan mutunci. Don haka, ina yi masu fatan alheri da addu’ar Allah ya ba su zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba.”
Game da halin da ƙasa take ciki, yadda ake samun matsalolin tsaro a sassa daban-daban, Oba Adekunle Makama ya yi kira ga al’ummar ƙasa da su sanya ido sosai a yankunansu, inda ya ce idan sun ga wani abu na rashin tsaro, su sanar wa hukuma kuma su riƙa ba jami’an tsaro haɗin kai a aikinsu.
“Su kuma masu mulki, ina kira a gare su, da su ji tsoron Allah, su yi mana adalci. Idan suka yi mana adalci, da Kudu da Arewa, Gabas da Yamma sai a samu zaman lafiya da ci gaba,” in ji mai martaba.
Ga malaman addini kuwa, Oba Adekunle ya ce: “Ina kira a gare ku, ku ci gaba da wa’azi da jan hankalin jama’a da ayoyin Allah amma ku kauce wa shiga lamarin siyasa. Mu a Kudu, malamai ba su tsoma baki a sha’anin siyasa.”
Haka kuma ya yi kira ga al’ummar ƙasa gaba ɗaya da su daina nuna wariya da ƙabilanci ga juna. “Mu yi koyi da rayuwar Janar Buratai, wanda shi cikakken ɗan kishin ƙasa ne, mai son mutane. Kudu da Arewa, Gabas da Yamma, kowa nasa ne. Dubi dai misalin yadda aka gudanar da bikin nan na ɗiyarmu, duk Najeriya an taru,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, “don haka, babu abin da ya fi zumunci, domin Manzon Allah (saw) ya yi kira da a yi zumunci. Saboda haka a ci gaba da zumunci.”
A ranar Asabar da ta gabata ce dai, aka gudanar da gagarumin bikin aure da hawan dawaki, wanda aka shirya domin taya murnar auren A’ishatu Tukur Buratai da Umar Abba Zoru. An gudanar da wannan babban taro ne a Gidan Gonar Tukur and Tukur Farms, da ke Gora, Jihar Nasarawa, inda fitattun baƙi daga sassa daban-daban na Najeriya da ma ƙasashen waje suka hallara domin taya amarya da ango murna.
__________













