• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, July 30, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

A Yayin Da Aka Kashe Janar Saura Wa Kuma Ya Rage?

TSOKACI

Danladi Z. Haruna by Danladi Z. Haruna
June 14, 2026
in Gizago
0
A Yayin Da Aka Kashe Janar Saura Wa Kuma Ya Rage?

Allah ya ji ƙan Manjo-Janar Rabe Abubakar

27
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

A Yayin Da Aka Kashe Janar Saura Wa Kuma Ya Rage?

Daga Danladi Z. Haruna
__________
Labarin rasuwar tsohon jami’in tsaro kuma tsohon mai magana da yawun rundunar tsaro ta Najeriya, Manjo-Janar Rabe Abubakar (mai ritaya), yayin da yake tsare a hannun ‘yan bindiga, babban rashi ne mai karya zuciya, wanda ya jefa ɗaukacin Arewa da ma Najeriya baki ɗaya cikin juyayi da alhini.

Related posts

Ko Yaya Za A Fassara Wannan Kallon?

Ko Yaya Za A Fassara Wannan Kallon?

July 30, 2026
Saƙon Godiya Da Bangajiya

Saƙon Godiya Da Bangajiya

July 22, 2026

Janar Rabe, wanda ya fito daga Ƙaramar Hukumar Batsari da ke Jihar Katsina kuma ya kwashe shekaru yana yi wa ƙasarsa hidima da yaƙar ta’addanci, ya rasu ne sakamakon matsalolin rashin lafiya na ciwon suga da hawan jini.

Allah ya ji ƙan Manjo-Janar Rabe Abubakar

Kamar yadda sanarwa daga Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar, Janar ɗin ya rasu ne a yayin da yake tsare a sansanin ‘yan bindigar, bayan o sace shi da suka yi, tare da matarsa, tun ranar 30 ga watan Mayu na bana, a kan hanyar Marabar Musawa zuwa Kafinsoli.

Wannan mummunan lamari, wanda Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar, babban saƙo ne da ke nuni da irin barazanar da kowanne ɗan ƙasa ke ciki a yau; inda hatta ƙwararrun dakarun soja da suka yi hidimar kare ƙasarsu a tsawon rayuwarsu, ba su tsira daga barazanar tsaro ba.

A wani bidiyo, wanda ya karaɗe kafafen sada zumunta, an nuno Janar ɗin, kafin rasuwarsa, inda yake roƙon a kawo masa ɗauki saboda halin rashin lafiya, ya sa zukata sun karaya. Kuma ya nuna yadda Arewa ta zama fagen fama – babu wanda ya isa ya bugi ƙirji ya ce zaune lumui ake.

Ga shi dai manyan masu faɗa a ji da manyan jami’ai masu ƙwarewa suna gangarawa a hannun mutanen da ko “alu ambaki” ba su iya ba, ballantana “abacada.”

Ga mai hankali, ya san cewa yanzu ba lokacin zargi ba ne. Ba lokaci na surutu mara amfani ba ne. Ba kuma lokaci ne da shugabanni za su cigaba da zabga ƙarya da labarai marasa kan gado ba.

Lokaci ne da Arewa da ma Najeriya baki ɗaya suke buƙatar gaggawar mafita, musamman ta hanyar sauya dabarun zamantakewa. Lokaci ne da gwamnati za ta samar da dabarun yaƙi na zamani.

Masu wannan aika-aika sun nuna a zahiri cewa, tuni sun bijire wa tsofaffin hanyoyin da aka saba da su na yaƙin kuma ba sa buƙatar sulhu ko lallaɓawa.

Ya zama dole a ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki kan masu bai wa dakarun ta’addanci bayanai (informants). Wajibi ne shugabannin Arewa na siyasa, na gargajiya da na addinai su ajiye bambance-bambancensu gefe guda, domin ceto yankin daga rugujewar tattalin arziki da yunwar da ke tafe saboda rashin zaman lafiya.

Muna roƙon Allah ya ji ƙan Janar Rabe Abubakar da sauran bayin Allah da suka rasa rayukansu, ya bai wa iyalansa juriya, sannan ya tseratar da matarsa da ke hannunsu. Allah ya dawo da zaman lafiya mai ɗorawa a ƙasarmu.

Malam da Malama masu karatun wannan tsokaci, Idan har kun damu da halin da Arewa take ciki, ku danna maɓallin “Share” domin yaɗa wannan saƙon, ya kai ga kunnuwan masu ruwa da tsaki a gwamnati.
__________

Previous Post

Inna Lillahi… We Lost Gen. Rabe

Next Post

Deepening Security Crisis: Buratai Calls for Emergency Measures

Related Posts

Ko Yaya Za A Fassara Wannan Kallon?
Gizago

Ko Yaya Za A Fassara Wannan Kallon?

July 30, 2026
Saƙon Godiya Da Bangajiya
Gizago

Saƙon Godiya Da Bangajiya

July 22, 2026
MALUMFASHI: Yau Haƙuri Ya Yi Rana
Gizago

MALUMFASHI: Yau Haƙuri Ya Yi Rana

July 21, 2026
Next Post
Deepening Security Crisis: Buratai Calls for Emergency Measures

Deepening Security Crisis: Buratai Calls for Emergency Measures

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Kafafen Yaɗa Labarai Su Ne Manyan Dirkokin Da Ke Ɗauke Da Nagartacciyar Dimokiraɗiyyarmu – Minista

Kafafen Yaɗa Labarai Su Ne Manyan Dirkokin Da Ke Ɗauke Da Nagartacciyar Dimokiraɗiyyarmu – Minista

December 20, 2023
Jiya Lamine Yamal Ya Yi Wasan Kura Da Mbappé

Jiya Lamine Yamal Ya Yi Wasan Kura Da Mbappé

July 15, 2026
KWATAM HUBA HALIMA TAHIR: Tattaunawa Da Fitattar ‘Yar Jarida Basarakiya

KWATAM HUBA HALIMA TAHIR: Tattaunawa Da Fitattar ‘Yar Jarida Basarakiya

August 19, 2023
A Review of Boko Haram and other Security Challenges in Nigeria

A Review of Boko Haram and other Security Challenges in Nigeria

April 20, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Ko Yaya Za A Fassara Wannan Kallon?
  • Janar Buratai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne – Oba Adekunle Makama
  • General Buratai Is a Great Patriot — Oba Adekunle Makama

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Ko Yaya Za A Fassara Wannan Kallon?

Ko Yaya Za A Fassara Wannan Kallon?

July 30, 2026
Janar Buratai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne – Oba Adekunle Makama

Janar Buratai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne – Oba Adekunle Makama

July 30, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.