Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

__________
Ya zuwa yanzu dai Fasto Emmanuel Sunday Garba, ɗan ƙungiyar Hausawan Bogi kuma ɗan Ba-Zata ya shiga tsilla-tsilla, yana ta wasan ɓuya, tun bayan da bidiyonsa ya bayyana, yana cin zarafin Manzon Tsira, Badadin Allah, Annabi Muhammadu (saw).
Ya zuwa yanzu dai, kamar yadda na samu labari daga Sheikh Adam Ashaka shugabannin ƙungiyar ‘yan Ba-Zata sun yi masa biza, wataƙila za su fitar da shi daga ƙasar nan. Wannan yake nufin ya tsorata da MATAKIN DA AL’UMMAR MUSULMI za su ɗauka a kansa, kamar yadda suka yi alƙawari.
Da ma a kwanakin baya na taɓa shaida maku cewa, tun da kuka ga Hausawan Bogi suna zagin Mujaddadi Ɗanfodiyo da sauran manyan malaman Musulunci, to inda suka nufa shi ne BABBAR DANGA – wato nan gaba za su koma kan zagin Manzon Allah (saw). Yalai kuwa, shi ne Fasto Emmanuel Sunday Garba ya fara yanzu.
Lallai kam ya kamata hukumomi su ɗauki matakin da ya dace. Haka kuma ya kamata al’ummar Kirista, abokan zamanmu su kiyaye mutumcin al’ummar Musulmi, su daina gigin taɓa martabar Manzon Allah (saw). Haka kuma ya kamata su fahimta da cewa, Al’ummar Musulmin Duniya gaba ɗaya suna daraja Yesu Kiristi, Annabi Isa (alaihis salam). Hasalima, duk Musulmin da bai yarda da Annabi Isa ba, to ya fita daga Musulunci.
Muna roƙon Allah Ya kawo mana fahimta da zaman lafiya da juna. Allah sa mu dace, Amin.
__________













