RAMADAN KARIM: 30-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Yau Alhamis, Allah ya nuna mana rana ta 30 a Ramadan. Yau ma ga nasiharmu:
Jama’a, yau nasiharmu ita ce, mu fahimta da cewa duniya dai ba gidan zama ba ne na har abada. Duniya gida ne na jarabawa, gida ne da Allah ya kawo ɗan Adam, ba don komai ba sai don ya bauta masa. Don haka, mu yi ƙoƙari mu aikata alheri a duniya, domin mu girbi alheri a lahira.
Allah (swt) a cikin Suratul Ƙasas 28:77 ya gargaɗe mu da cewa: “Kuma ka nemi (lada) gidan lahira da abin da Allah ya ba ka, kada kuma ka manta da rabonka a duniya. Kuma ka yi kyautatawa kamar yadda Allah ya yi maka kyautatawa. Kada kuma ka nemi ɓarna a cikin ƙasa. Lalle Allah ba ya son masu ɓarna.”
Haka kuma Annabi Muhammadu (saw) a Hadisin Imam Bukhari mai lamba 6416, ya ce: “Ku kasance a duniya kamar baƙo.”
Ya Allah, ka sanya mu cikin masu rabo a duniya da lahira. Ka ba mu ikon bauta maka yadda kake so kuma ka sanya mu cika da ingantaccen imani, idan lokacinmu ya zo. Amin-Summa-Amin.
__________













