RAMADAN KARIM: 23-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Yau Alhamis, Allah ya nuna mana rana ta 23 a Ramadan. Yau ma ga nasiharmu:
Jama’a, barka da wannan lokaci. A yau za mu yi jan hankali ne game da rayuwar duniya. Lallai ne mu sani cewa wannan rayuwar mai ƙarewa ce. Don haka kada mu sake mu shagaltu da ita. Mu zage mu aikata alheri, domin mu samu babban guzurin tafiya lahira, inda can ne gidanmu na zama ba har abada.
Allah (swt) a cikin Alkur’ani mai girma, Suratul Hadid 57:20, ya bayyana cewa: “Rayuwar duniya wasa ce kawai…” Haka kuma, Manzon Allah (saw), a Hadisin Muslim mai lamba 2956, ya ce: “Duniya kurkuku ce ga muminai…”
Ya kamata mu yi taka-tsan-tsan da rayuwar duniya. Allah ya sa mu cika da imani. Amin-Summa-Amin.
__________













