RAMADAN KARIM: 16-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Yau Alhamis, Allah ya nuna mana rana ta 16 a Ramadan. Ga nasiharmu ta yau:
Ya ‘yan uwa, mu sani cewa akwai babban alheri ga mutumin da ya kasance mai taimakon ɗan uwansa. Kuma a matsayinmu na mutane, muna da buƙatar taimako daga junanmu ta fuskoki daban-daban. Don haka mu lizimci taimako, a duk lokacin da muka gamu da masu buƙatar taimako daga gare mu.
Allah (swt) a cikin Suratu Ma’idah 5:2, ya ce: “Ku taimaki juna a kan alheri.” Haka ma Manzon Allah (saw), a Hadisin Muslim mai lamba 2699, an ruwaito yana cewa: “Allah yana taimakon bawa muddin bawan yana taimakon ɗan uwansa.”
Ya Allah ka ba mu ikon taimako, a duk lokacin da muke da iko. Amin-Summa-Amin.
__________













