KTSTA: HARKAR SUFURI A HANNUN GWANI (1)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Sufuri na ɗaya daga cikin al’amura mafiya muhimmanci a rayuwar al’umma. Duk wani al’amari na rayuwar al’umma yana da kaso mafi girma a harkar sufuri – misali, noma da kiwo don abinci, ilimi, kiwon lafiya da sauransu.
La’akari da muhimmancin harkar ta sufuri ne ya sanya gwamnati ta samar da hukuma sukutum domin bunƙasa harkar. Wannan hukuma kuwa ita ce – KTSTA – Katsina State Transport Authority (Hukumar Sufuri ta Jihar Katsina).
Tun da farko, an kafa hukumar ce a shekara ta 1987, lokacin da aka ƙirƙiro Jihar Katsina daga tsohuwar Jihar Kaduna, zamanin mulkin soja na Janar Ibrahim Badamasi Babangida. A ƙarƙashin Gwamnan mulkin soja na farko a jihar, Janar Abdullahi Sarki Mukhtar ne aka kafa Hukumar. Ya yi mulki daga shekarar 1987 zuwa 1988.

Hukumar ta KTSTA ta dakatar da harkokinta a shekarar 1990 bisa wasu dalilai, inda gwamnati a ƙarƙashin Gwamnan mulkin soja, Kanar Yahaya J. Madaki na lokacin ya rufe ta.
A shekarar 1992 ce aka farfaɗo da Hukumar KTSTA, a ƙarƙashin Gwamna Alhaji Sa’idu Barda – Gwamnan Jihar Katsina na farko a mulkin farar hula. Kamar yadda tarihi ya tabbatar, farfaɗo da hukumar ya samo asali ne bisa shawarar Gwamna Aminu Bello Masari, wanda a lokacin shi ne Kwamishinan Ma’aikatar Ayyuka, Gidaje da Sufuri.

Tun daga lokacin, hukumar ta ci gaba da gudanar da harkokinta. An samu ƙalubale da matsaloli masu tarin yawa a harkokin hukumar. A haka har aka zo kan Gwamnatin Alhaji Aminu Bello Masari. Shi ne ya miƙa mulkin gudanarwar KTSTA ga hannun Malam Haruna Musa Rugoji, a watan Nuwamba na shekarar 2018.

Ya zuwa wannan lokaci da muke haɗa wannan rahoto, Malam Rugoji ne ke shugabancin wannan hukuma – mutumin da ya kasance ƙwararre kuma masanin harkokin sufuri.

Shin wane ne Malam Haruna Musa Rugoji? Ku biyo mu a rahoto na gaba, in sha Allah.
__________













