• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, April 18, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

SHIRIN GWAMNA ABBA GIDA-GIDA NA RABA TALLAFIN AWAKAN KIWO YANA KAN DAIDAI

TSOKACI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
January 23, 2025
in ENGLISH
0
SHIRIN GWAMNA ABBA GIDA-GIDA NA RABA TALLAFIN AWAKAN KIWO YANA KAN DAIDAI

Shirin Tallafin Dabbobin Kiwo Ga Matan Karkara

59
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

SHIRIN GWAMNA ABBA GIDA-GIDA NA RABA TALLAFIN AWAKAN KIWO YANA KAN DAIDAI

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (10)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (10)

April 12, 2026
Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles

Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles

April 5, 2026
Yayin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ke raba asali domin kiwo

 

A ‘yan kwanakin nan ne labari ya cika kafafen soshalmidiya, wasu suna suka da caccakar Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf saboda ya ƙaddamar da shirin bayar da tallafin dabbobin kiwo ga matan karkara, da nufin bunƙasa noma da kiwo a hannu ɗaya da kuma rage raɗaɗin talauci da ƙarfafa ƙananan sana’o’i ga mata a karkara da ɗaukacin jihar, a ɗaya hannun.

Kamar yadda labari ya tabbatar, Gwamna Gida-Gida ya kashe Naira biliyan 2.3 wajen ƙaddamar da shirin, inda aka raba adadin awakai 7,158 ga mata 2,386.

Gwamna Abba Kabir Yusuf

Haka kuma, kamar yadda Daraktan Watsa Labarai na Gwamnan, Malam Sanusi Bature Dawakin Tofa ya bayyana, ya ce akwai kuma shiri na gaba, inda gwamnan zai raba shanu guda 1,342 da raguna 1,822 ga wasu rukunin matan daban.

Maimakon sukar wannan shiri, kamata ya yi mu duba manufarsa da sakamakon da zai haifar wajen gina rayuwar al’umma.

Ɗauki misalin rayuwar mutanen karkara, musamman mata, yadda suke cikin talauci da ƙuncin rayuwa. Ta wace hanya za ka iya sauƙaƙa kaifin matsalolinsu? Shi ne ta hanyar inganta sana’arsu. Kamar yadda wata azancin maganar mutanen China take cewa,
“Ka koya wa mutane yadda ake kamun kifi, shi ya fi alheri da ka riƙa kama kifin kana raba masu.”

Sanusi Bature Dawakin Tofa

Yanzu misali, an raba wa mata fiye da 2000 awakai sama da 7000. Idan suka kiwata su kuma Allah ya albarkace su, kafin shekara ta kewayo guda nawa za su koma? Babu mamaki, cikin matan nan daga nan wata za ta tara garke. Daga nan wata za ta zama attajira, saboda sun saba da kiwo kuma za su ririta abin yadda zai yaɗu.

Nan fa ake ta kukan cewa gwamnoni sun ƙyale mutanen karkara, suna ta gina gadoji a manyan birane. Idan ba ta wannan ƙaramar hanyar ba, ta yaya ake zaton mutanen karkara za su amfana da tallafin gwamnati?

Wasu kuma suna zargin wai akwai aringizo wajen sayen dabbobin. Ni kuwa nake ganin a wannan yanayin da muke ciki, idan ɗan siyasa ya ga damar ɗibar kuɗi, zai ɗiba ne ko nawa ya ga dama, koda bai shigo da wannan tsarin ba. Don haka Ni na fi kallon tasirin tsarin, fiye da yawan kuɗin da ake ikirarin an kashe.

Wata da ta amfana da tallafin akuya

Ni a ganina, maimakon wasu da suke ta sukar shirin, kamata ya yi a yaba wa Gwamna kuma a ƙarfafa masa gwiwa, sannan a buƙaci ya faɗaɗa shirin ya shafi ƙanana da matsakaitan ‘yan kasuwa da masu sana’o’in hannu. Haka kuma, ya kamata su ma sauran gwamnonin Arewa su ɗauki wannan salo na ƙarfafa noma da kiwo da ƙananan sana’o’i ga talakawa, musamman na karkara.

Ni dai a nan, ina yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa wannan shiri na bunƙasa tattalin arziƙin talakawan karkara. Ina fatan zai ci gaba da gudanar da tsarin a kowace shekara, yadda al’amarin zai isa ga mutane masu yawa. Allah Ya sa mu dace, Amin.

Previous Post

Gasar Kano-2024: Nasarar Da Na Samu Ta Canja Mani Tunani Game Da Rubutu – Zakariyya

Next Post

ILLOLI DA MATSALOLIN DA ƘUNGIYOYI DA ƘUNGIYANCI KE HAIFAR WA MUSULUNCI DA MUSULMI

Related Posts

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (10)
ENGLISH

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (10)

April 12, 2026
Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles
ENGLISH

Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles

April 5, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (9)
ENGLISH

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (9)

April 4, 2026
Next Post
ILLOLI DA MATSALOLIN DA ƘUNGIYOYI DA ƘUNGIYANCI KE HAIFAR WA MUSULUNCI DA MUSULMI

ILLOLI DA MATSALOLIN DA ƘUNGIYOYI DA ƘUNGIYANCI KE HAIFAR WA MUSULUNCI DA MUSULMI

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

ADC: The Wind of Change Has Come – Dr. Aminu Waziri

ADC: The Wind of Change Has Come – Dr. Aminu Waziri

July 7, 2025
Tinubu Ya Ƙwace Muƙamin Minista Daga Maryam Shatty

Tinubu Ya Ƙwace Muƙamin Minista Daga Maryam Shatty

August 4, 2023
WILL ATIKU’S EXIT FROM THE PDP BRING HIM VICTORY IN 2027?

WILL ATIKU’S EXIT FROM THE PDP BRING HIM VICTORY IN 2027?

July 19, 2025
Mu Ji Tsoron Allah

Mu Ji Tsoron Allah

April 17, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Ko Me Ya Sa Manyan Mata Ke Auren Yara?
  • Mu Ji Tsoron Allah
  • Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Ko Me Ya Sa Manyan Mata Ke Auren Yara?

Ko Me Ya Sa Manyan Mata Ke Auren Yara?

April 18, 2026
Mu Ji Tsoron Allah

Mu Ji Tsoron Allah

April 17, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.