• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, May 3, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

Taron editoci: Tinubu na so a riƙa yaɗa kyawawan labarai don jawo zuba jari a Nijeriya

Daga Wakilinmu by Daga Wakilinmu
November 16, 2023
in Labarai
0
Taron editoci: Tinubu na so a riƙa yaɗa kyawawan labarai don jawo zuba jari a Nijeriya

Alhaji Mohammed Idris, Ministan Yaɗa Labarai

14
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Taron editoci: Tinubu na so a riƙa yaɗa kyawawan labarai don jawo zuba jari a Nijeriya

 

Related posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nemi kafafen yaɗa labarai da su taimaka wajen bada labarai da bayanai da za kyautata matsayin Nijeriya a idon duniya ta yadda masu zuba jari za su samu ƙwarin gwiwar saka dukiyar su a ƙasar wanda hakan zai taimaka wa cigaban tattalin arzikin ta.

Shugaban ya yi wannan kiran ne a saƙon sa da Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya karanta a madadin sa a wajen buɗe Babban Taro na 19 na Dukkan Editocin Nijeriya wanda Ƙungiyar Editocin Nijeriya (NGE) ta shirya a Uyo, Jihar Akwa Ibom, a ranar Laraba.

A cikin sanarwar da mai taimaka wa ministan na musamman a fagen yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim, ya bayar a Abuja, ya ruwaito Tinubu ya na faɗin: “An san rawar da ku ke takawa a matsayin tushen farko na labarai kuma masu wayar da kan al’umma game da abubuwan da ke faruwa a fagen tattalin arziki. Don haka bada rahotanni a kan kari waɗanda babu ƙarin gishiri cikin su ya na taimakawa ga masu sana’o’i su yanke shawarar da ta dace, kuma ya na samar da kyakkyawan yanayi don haifar da cigaban ƙasa.

“Ina kira a gare ku da ku samar da kyawawan labarai waɗanda za su bada ƙwarin gwiwa ga masu zuba jari kuma su jawo irin jarin da zai inganta haɓakar tattalin arziki a wannan ƙasa tamu.

“Rawar da kafafen watsa labarai ke takawa wajen samar da kyakkyawan yanayin hada-hadar kasuwanci ta na taimakawa ga daidaita harkar kasuwanci.”

Shugaban ƙasar ya ce samar da kyakkyawan musayar ra’ayi kan yadda za a inganta tsarin tattalin arzikin ƙasa wani abu ne da gwamnatin sa ta yi amanna da shi, kuma ya yi kira da a samu haɗin kan editocin wajen ƙoƙarin yin tattaunawa daidai da Manufar Sabuwar Alƙibla ta gwamnatin sa.

Tinubu, wanda ya yi la’akari da matsalolin da ake ciki waɗanda janye tallafin man fetur ya haifar, ya ce gwamnatin sa ta na ɗaukar duk wani mataki da ya dace don rage raɗaɗin da ake ji, ta hanyar tsare-tsare da aka yi da za su kawo sauƙi a cikin ƙanƙanen lokaci, a yayin da ƙasar ta ke jiran ta ci moriyar abin a nan gaba.

Ya lissafa wasu daga cikin tsare-tsaren rage raɗaɗin da su ka haɗa da ƙarin albashi na N35,000 a kowane wata har tsawon watanni shida, wanda ƙari ne kan albashi mafi ƙaranci na Gwamnatin Tarayya; da kafa Asusun Tallafin Ayyuka ga Jihohi don zuba kuɗi a muhimman sassa wanda zai samar da yanayin da zai bunƙasa harkokin kasuwanci, da kuma ƙaddamar da shirin sawo motocin safa-safa samfurin CNG na naira biliyan 100, masu aiki da hasken rana, da kuma kafa Kwamitin Shugaban Ƙasa don tabbatar da aiwatar da shirin.

Ya ce: “Da yake an rattaba hannu kan dokar Ɗorin Kasafin Kuɗi na 2023, mun kammala matakan da za mu bi mu fara biyan kuɗin Tiransifar Tsabar Kuɗi N25,000 ga kowane mutum a cikin mutum miliyan 15 mafi fatara da kuma gidaje waɗanda su ka fi buƙata a Nijeriya, har tsawon wata uku.

“An bada umurnin shugaban ƙasa na fitar da tan 200,000 na hatsi daga rumbunan musamman na gwamnati ga gidajen jama’a a jihohi 36 da gundumar Abuja a farashi mai rahusa, da tan 225,000 na takin zamani, da iri, da sauran kayan aiki ga manoma.”

Tinubu ya ce a dalilin faɗuwar tarbiyya da aka samu a tsawon lokaci, wanda ya jawo raguwar mutunta ƙasa, Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai ta Tarayya (FMINO) ta na nan ta na tsara sauya labarin da ake yaɗawa game da ƙasar nan ta hanyar aiwatar da wani gagarumin shirin wayar da kan al’umma wanda nufin sa ya samar da haɗin kai, kishin ƙasa, da saka shauƙin son al’adun mu a zukatan ‘yan Nijeriya.

Shugaban ƙasar ya yi kira ga dukkan editocin kafafen yaɗa labarai da su yaƙi muguwar ɗabi’ar yaɗa labaran ƙanzon kurege, da labaran yaudara, da labaran ƙarya, masu yin barazana ga al’umma, ya ce su riƙa binciken gaskiyar lamari, da bada labarai cikin hankali da natsuwa, da inganta ilimin aikin jarida da ilimin kafafen zamani.

Ya yaba wa iyayen da su ka kafa ƙungiyar ta NGE, bisa jagorancin marigayi Alhaji Lateef Kayode Jakande, wanda zaƙaƙurin ɗan jarida ne da ake girmamawa kuma har ya riƙe muƙamin Gwamnan Jihar Legas, wanda a cikin 1961, shi da wasu, su ka kafa ƙungiyar, su ka bada gudunmawa ga cigaban ƙasa ta fuskar zamantakewa da siyasa, musamman wajen ‘yanto Nijeriya daga baƙin mulki irin na soja har aka samar da mulkin dimokiraɗiyya.

Previous Post

SAI AN YI DA GASKE: Littafin Wasan Kwaikwayo A Mizanin Nazari Da Sharhi

Next Post

DRUG KINGPIN: NDLEA Arrests Prison Escapee 7 Years After

Related Posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi
Labarai

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina
Labarai

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

February 13, 2026
Next Post
DRUG KINGPIN: NDLEA Arrests Prison Escapee 7 Years After

DRUG KINGPIN: NDLEA Arrests Prison Escapee 7 Years After

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Matsalar Tsaro A Najeriya: Madalla Da Majalisar Dokokin Amurka

Matsalar Tsaro A Najeriya: Madalla Da Majalisar Dokokin Amurka

November 26, 2025
Daura Birnin Bayajidda: Janar Buratai Da Ayarinsa Sun Ziyarci Buhari Da Sarki

Daura Birnin Bayajidda: Janar Buratai Da Ayarinsa Sun Ziyarci Buhari Da Sarki

June 4, 2023
BAKIN JAƁA (3)

BAKIN JAƁA (3)

September 9, 2025
Ƙuncin Rayuwa: Matasa Ku Tashi Ku Nemi Ilimi Da Sana’a – In Ji MAK

Ƙuncin Rayuwa: Matasa Ku Tashi Ku Nemi Ilimi Da Sana’a – In Ji MAK

August 15, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)
  • General Buratai (A Poem)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

April 27, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.