HAƊARIN MOTA: Gizagawan Najeriya Sun Yi Dubiya Ga ‘Yar Uwa Ruƙayya Jos
~~~~~~~
Gizagawan Najeriya sun kai ziyarar dubiya zuwa ga Bagizagiya Malama Ruƙayya Jos, Jihar Filato.
Malama Ruƙayya, wacce a kwanakin baya ta gamu da ibtila’in karaya har uku, a sakamakon haɗarin mota, a halin yanzu take jinya a gida.
Gizagawan Najeriya, reshen Jihar Filato, a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Gizagawa na jihar, Muhammed da tsohon Mai Ladabtarwa na Ƙasa, Abubakar Hamisu Yankatsari ne suka wakilci ɗaukacin Gizagawan Najeriya baki ɗaya wurin dubiya da miƙa tallafin kuɗi.
An miƙa wa mai jinyar ₦31, 000, adadin kuɗin da Gizagawan suka haɗa daga junansu, a matsayin tallafi.
An yi zumunci tare da addu’ar Allah Ya ba ta lafiya. Haka kuma an yi godiya ga ɗaukacin Gizagawan Najeriya, da fatan Allah Ya saka wa kowa da alheri.
~~~~~~~














