RAMADAN KARIM: 24-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Yau Juma’a, Allah ya nuna mana rana ta 24 a Ramadan. Yau ma ga nasiharmu:
A yau mun shiga Juma’a ta ƙarshe a Ramadan na bana kuma za mu tunatar da juna ne dangane da abin da ya shafi sauƙi da sauƙaƙawa. Yana daga cikin halaye masu kyau kuma abin so gare mu, mu kasance masu sauƙi da sauƙaƙawa ga juna a cikin al’amuranmu na yau da kullum. Idan za ka saya ko za ka sayar, ka sauƙaƙa.
Allah (swt) a cikin Alkur’aninsa mai girma, a Suratul Baƙara 2:185, yana cewa: “Allah yana nufin sauƙi gare ku.” Haka shi ma Manzon Allah (saw), a Hadisin Bukhari mai lamba 69 da Muslim, Hadisi mai lamba 1734 yana cewa: “Ku yi sauƙi, kada ku tsananta.”
Muna roƙon Allah ya sauƙaƙa mana kuma ya sanya mu zama masu sauƙaƙa wa juna. Allah ka yafe mana, ka sanya mu daga cikin ‘yantattu a cikin wannan wata na Ramadan mai albarka da bayansa. Amin-Summa-Amin.
__________













