RAMADAN KARIM: 17-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Yau Juma’a, Allah ya nuna mana rana ta 17 a Ramadan. Ga nasiharmu ta yau:
Tafiya sannu-sannu kwana nesa! A yau nasiharmu tana nuni ne zuwa ga haƙuri da muhimmancinsa. Haƙuri babbar halayya ce ta ƙwarai, mai haifar da alheri a kowane lokaci. Masu iya magana sun ce, mahaƙurci mawadaci ne.
Allah (swt) a Suratul Baƙara 2:153 ya ce: “Ku nemi taimako da haƙuri da salla.” Haka ma a Hadisin Muslim mai lamba 223, an ruwaito Manzon Allah (saw) yana cewa: “Haƙuri haske ne.”
Muna roƙon Allah ya sanya mu cikin masu haƙuri kuma ya wadata mu da albarkar haƙuri. Amin-Summa-Amin.
__________













