RAMADAN KARIM: 07-1447

__________
‘Yan uwa, ina yi maku sallama irin ta Musulunci, Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuhu. Bayan haka, a yau Talata, Allah ya nuna mana rana ta 7 a Ramadan, don haka za mu amfana da juna a wannan rana da ‘yar nasiha:
‘Yan uwa, yau nasiharmu tana kira ne a gare mu da mu so juna, mu kasance masu taimakon juna a dukkan halin da muke ciki. Allah (swt) a Suratul Hashr 59:9, ya ce: “…suna fifita wasu a kan kansu.” Hakan yake nuna siffar mutanen kirki, masu yi wa al’umma hidima ba tare da la’akari da wani bambanci ba.
Haka ma a Bukhari, a Hadisi mai lamba 13 da Muslim, a Hadisi mai lamba 45, sun ruwaito Manzon Allah (saw) yana cewa: “Ya so wa ɗan uwansa abin da yake so wa kansa.” Ma’ana, ana kira ne ko kuma nuni ga mutane da su kasance masu kula da taimakon juna.
A duk lokaci da ka so wa ɗan uwanka abin da kake so wa kanka, shi ma ya so maka abin da yake so wa kansa, yaya kake ganin rayuwa za ta kasance? Tabbas, za a samu zaman lafiya da kwanciyar hankali da ƙaunar juna, domin kuwa babu wanda zai so wa kansa sharri, sai alheri.
Ya Allah, ka saita zukatanmu, mu kasance masu ƙauna da taimakon juna a kowane lokaci. Amin!
__________













